Matar ta ce mijin ya kai ƙorafi ga 'yan sanda yana zarginta da kwashe kayansa, amma takardun shaidar biyan kuɗin kayayyakin ta hanyar tsarin ajiyar kuɗin ma'aikatarsu sun nuna cewa ita ce ta saya su da albashinta.
A cewar Majalisar Dattawa, gyaran dokar na da nufin karfafa aiwatar da dokokin hanya, rage hadurran mota da kuma inganta tsaron matafiya a fadin Najeriya.
Ya ce noma ya taba zama abin da ya ba miliyoyin 'yan Najeriya damar samun abin dogaro da kai, yana mai kira ga gwamnati, masu zuba jari da matasa su kara mayar da hankali kan bunkasa bangaren.
"Jagoranci na nufin daukar matakai masu wahala. Kuma jagoranci ba na mutane masu son faranta wa kowa rai ba. Irin wadannan mutane su fi dacewa da sayar da cakulan ko ice cream."
Ya kuma yi kira ga 'yan Najeriya da kada su ɗora wa Peter Obi alhakin juyin mulkin soja na shekarar 1966, yana mai cewa Obi ba shi da wata alaƙa da abin da ya faru a lokacin.
wasu sun bayyana damuwa cewa matakin na iya haifar da rashin tabbas ga masu zuba jari, tare da rage damar bunƙasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi a yankunan da abin ya shafa.
Ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta fi mayar da hankali kan bunƙasa ilimi, samar da ayyukan yi da koyar da matasa sana’o’in zamani, maimakon dogaro da rabon kuɗi.