Daga Wakiliya:
WAKILIYA: Wata mata ta bayyana yadda rikici kan kuɗin gādon kusan Naira miliyan 35 da mahaifinta ya bari ya jawo rugujewar aurenta, lamarin da ya kai ga ta bar gidan mijinta tare da shigar da ƙarar saki a kotu.
A cewar mai bayar da labarin kuma kwararriyar mai shiga tsakanin ma’aurata, Bilkisu Yahaya, bayan ta sanar da mijinta cewa tana son sayen fili, mota, yin karatun digiri na biyu da kuma saka sauran kuɗin a kasuwancinta, mijin ya buƙaci ta miƙa masa kuɗin, yana mai cewa hakan ne ya dace da matsayinsa na miji.
Ta ce daga baya mijin da iyayensa sun matsa mata lamba su nemi ta canja masa duk kuɗin gādon, lamarin da ya sa ta fice daga gidan tare da ɗanta, kafin daga bisani ta koma ta kwashe kayayyakin da ta ce ta saya da kuɗinta.
Matar ta ce mijin ya kai ƙorafi ga ‘yan sanda yana zarginta da kwashe kayansa, amma takardun shaidar biyan kuɗin kayayyakin ta hanyar tsarin ajiyar kuɗin ma’aikatarsu sun nuna cewa ita ce ta saya su da albashinta.
Ta ce daga baya ta shigar da ƙarar saki, yayin da mijin ya fara neman sulhu, yana cewa bai yi nufin raba auren ba.
Sai dai Wakiliya ba ta iya tabbatar da wannan labari daga ɓangarorin biyu ba, kuma ana ci gaba da sauraron shari’ar a kotu.





