Haɗakar Obi da Kwankwaso na fuskantar ƙalubale – Buba Galadima

Daga Wakiliya
Jigo a jam’iyyar Nigeria Democratic Co

ngress (NDC), Buba Galadima, ya amince cewa ana fuskantar wasu ƙalubale wajen yunƙurin samar da haɗakar takarar shugaban ƙasa tsakanin Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso.

Galadima ya bayyana haka a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce duk da matsalolin da ake fuskanta, ba su kai matsayin da ba za a iya magance su ba.

“Muna da matsaloli da dama, amma ba matsalolin da ba za a iya shawo kansu ba ne. Za mu shawo kansu,” in ji Galadima.

Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da kada su ɗora wa Peter Obi alhakin juyin mulkin soja na shekarar 1966, yana mai cewa Obi ba shi da wata alaƙa da abin da ya faru a lokacin.

A cewarsa, bai dace a riƙa hukunta mutane saboda abubuwan da wasu suka aikata ba, yana mai jaddada cewa haɗin kan ƙasa zai samu ne idan aka daina riƙe ƙiyayyar tarihi.

Galadima ya kawo misalin marigayi Chukwuemeka Odumegwu Ojukwu, wanda bayan yaƙin basasa aka yi masa afuwa, sannan ya dawo ya shiga harkokin siyasar Najeriya.

Ya kuma ce idan ana magana kan rikicin shekarar 1966, ya kamata a tuna cewa ba shugabannin Arewa kaɗai suka rasa rayukansu ba, domin ‘yan kabilar Igbo ma sun yi asara mai yawa.

A ƙarshe, Galadima ya jaddada cewa sulhu da tattaunawa ne hanya mafi dacewa wajen rage rabuwar kai da kuma gina haɗin kan Najeriya.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img