Labarai

“Duk wanda ya ce zai dawo da tallafin man fetur, yaudarar ’yan Najeriya yake yi” – Yari

“Bola Ahmed Asiwaju yana iya ƙoƙarinsa, kuma mun yi imanin shi ne mutumin da ya dace da wannan aiki a karo na biyu,” in ji Abdulaziz Yari.

Uba Sani ya ce Tinubu zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri’un Kaduna a 2027

Ku rubuta wannan ku ajiye, a yau. Ni Uba Sani nake gaya muku cewa Asiwaju zai samu kashi 70 zuwa 80 cikin 100 na ƙuri'un Kaduna a 2027,” in ji gwamnan.

Gwamnan Kaduna ya ce jihar na biyan N6.7bn na bashin da ta gada

“Muna biyan Naira biliyan 6.7 daga bashin da muka gada, kuma za mu ci gaba da biyan sa har zuwa 2048. Tun lokacin da na zama gwamna, ban ciwo ko sisi na sabon bashi ba,” in ji Sanata Uba Sani.

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

NELFUND: Mun raba wa ɗalibai miliyan 1.2 Naira biliyan 322 -Gwamnatin Tarayya 

Shugaba Tinubu ya ce ana buƙatar NELFUND ya kasance mai isasshen kuɗi kuma mai ɗorewa domin ci gaba da biyan buƙatun ɗaliban Najeriya.

Gwamnatin Tinubu za ta dawo da binciken mai a Arewa bayan tsaida aikin tun bayan hawansa mulki 

Shugaban RMAFC ya kuma ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na damuwa da yadda aikin ya tsaya, yana mai cewa an ba gwamnonin Bauchi da Gombe tabbacin cewa za a sake tura kayan aiki da ma'aikata domin ci gaba da aikin.

Duk wanda ya ce bai amfana da tallafin Tinubu ba, to baya Najeriya – Gwamnan Sokoto, Ahmed Aliyu 

Gwamnan ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su sake zaben Bola Tinubu a 2027, yana mai cewa yana da yakinin shugaban zai ci gaba da kawo sauyi a kasar.
- Advertisement -spot_img

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img