Duk wanda ya ce bai amfana da tallafin Tinubu ba, to baya Najeriya – Gwamnan Sokoto, Ahmed Aliyu
Daga Wakiliya
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya ce duk wani dan Najeriya da ya ce bai amfana da tallafin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba, to yana zaune ne a wajen Najeriya.
Ahmed Aliyu ya ce gwamnatin Tinubu ta aiwatar da shirye-shiryen tallafawa ’yan Najeriya, musamman marasa galihu, inda ya ambaci tallafin abinci, takin zamani kyauta da sauran tallafi.
“Idan ba ka ga tasirin ayyukan Tinubu ga ’yan Najeriya ba, to ba ka Najeriya,” in ji gwamnan.
Ya bayyana hakan ne ranar Lahadi a Jos, yayin wani taron karawa juna sani na kasa da kungiyar JIBWIS ta shirya kan siyasa da hadin kan kasa.
Ahmed Aliyu ya yi watsi da ikirarin ’yan adawa cewa gwamnatin Tinubu ba ta yi wani tasiri ba cikin shekaru uku, yana mai cewa irin wadannan kalamai farfaganda ne.
Gwamnan ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su sake zaben Bola Tinubu a 2027, yana mai cewa yana da yakinin shugaban zai ci gaba da kawo sauyi a kasar.
Taron ya samu halartar Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, Gwamnan Jigawa, Umar Namadi, da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin.





