Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Jami’an tsaron da aka tura aikin zaben Osun sun koka kan rashin biyansu alawus ɗin aikin

Daga Wakiliya

Wasu jami’an tsaro da aka tura aikin tabbatar da tsaro a zaɓen gwamnan jihar Osun na ranar 15 ga watan Agusta sun koka kan rashin biyan su alawus ɗin aikin zaɓen.

Jami’an da lamarin ya shafa sun haɗa da na Hukumar Tsaron Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC), Hukumar Shige da Fice (NIS), Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali (NCoS) da Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya.

Binciken jaridar The PUNCH ya nuna cewa jami’an ‘yan sandan da aka tura daga rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun karɓi N120,000 a matsayin alawus ɗin zaɓe, wanda aka biya su ta kashi biyu na N50,000 da N70,000, kwanaki kaɗan bayan zaɓen.

Sai dai wasu daga cikin jami’an sauran hukumomin sun ce har yanzu ba a biya su kuɗin aikin ba.

NSCDC ta ce ta tura jami’ai 10,210 zuwa jihar Osun, ciki har da jami’an ɗauke da makamai daga jihohin Kudu maso Yamma da wasu jihohi da suka haɗa da Kano, Nasarawa, Kogi, Kaduna da Abuja.

Haka kuma, kimanin jami’ai 300 daga Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali, akasari daga rundunar jihar Osun, aka tura aikin zaɓen.

Wani jami’in NSCDC da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa The PUNCH cewa sun isa Osogbo ranar 10 ga Agusta, inda aka sauke su a harabar wata makarantar sakandare kafin daga bisani a kai su hedikwatar hukumar.

Ya ce a lokacin da suke can sun koka kan rashin wadataccen kulawa, inda suka nemi a ba su kuɗin ciyarwa.

A cewarsa, an ba kowanne daga cikinsu N30,000 kafin a tura su ƙananan hukumomin da aka sanya su.

Sai dai ya ce tun bayan dawowarsa sansaninsa, ba a sake biyansa wani kuɗi ba.

Ya bayyana cewa yanayin da suka yi aikin zaɓen a ciki ya kasance mai wahala, lamarin da ya ce ya sa rashin biyan alawus ɗin ya ƙara musu takaici.

NSCDC ta ce ana biyan kuɗin

Jami’in hulɗa da jama’a na NSCDC, Babawale Afolabi, ya ce jinkirin biyan kuɗin ya samo asali ne sakamakon buƙatar tantance bayanan jami’an da aka tura aikin.

Ya ce hukumar ta fara biyan kuɗin bayan kammala tantance sunayen jami’an tare da kwamandojin jihohi.

A cewarsa, jami’an da ba su karɓi kuɗinsu ba su yi haƙuri, domin za a biya duk wanda ya shiga aikin zaɓen.

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali kuwa ta ce jami'arta mai magana da yawun hukumar, Jane Osuji, ba ta da masaniya kan ƙorafin, inda ta tura The PUNCH zuwa ga jami’in hulɗa da jama’a na rundunar Osun, Joel Oyedokun.

Sai dai ba a samu amsar kiraye-kirayen da aka yi masa ko saƙon WhatsApp da aka aika masa ba.

Haka kuma, jaridar ta ce ba ta samu damar jin ta bakin Hukumar Shige da Fice da Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya ba kan batun.

DA DUMI-DUMI

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Daga 1 ga Octoba WhatsApp zai fara cazar kuɗi kan saƙonnin da ake tura wa na kasuwanci

Sabon tsarin zai shafi kamfanoni da ke amfani da WhatsApp Business Platform, wadda aka fi sani da WhatsApp Business API, wajen tura saƙonni ga dimbin kwastomomi.

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

Kanun Labarai

Gwamnati za ta fara karɓar kuɗin wutar lantarki daga jami’o’i da asibitoci – Ministan Wuta

Wasu jami’o’i sun zo wurina domin su gode min bayan sun shafe shekara biyu suna amfani da wutar lantarki kyauta. Na ce musu, mun gode, amma lokacin kyautar ya ƙare. Yanzu za mu zo mu ƙaddamar da tsarin, kuma za ku biya kuɗin wutar lantarki,” in ji shi.

Gwamnatin Tarayya za ta sake duba tallafin karatu a ƙasashen waje

Dokta Alausa ya ce jim kaɗan bayan ya fara aiki a ma'aikatar, an gabatar masa da wani shiri da ya tanadi tura kusan ɗaliban Najeriya 100,000 zuwa Morocco domin karatun wasu darussa da ake koyarwa da Turanci, ciki har da aikin jarida da sadarwa.

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Daga 1 ga Octoba WhatsApp zai fara cazar kuɗi kan saƙonnin da ake tura wa na kasuwanci

Sabon tsarin zai shafi kamfanoni da ke amfani da WhatsApp Business Platform, wadda aka fi sani da WhatsApp Business API, wajen tura saƙonni ga dimbin kwastomomi.

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

NELFUND: Mun raba wa ɗalibai miliyan 1.2 Naira biliyan 322 -Gwamnatin Tarayya 

Shugaba Tinubu ya ce ana buƙatar NELFUND ya kasance mai isasshen kuɗi kuma mai ɗorewa domin ci gaba da biyan buƙatun ɗaliban Najeriya.

Hare-haren ’yan bindiga ya kashe mutane fiye da 10,000 cikin shekaru biyu na gwamnatin Tinubu – Amnesty

Amnesty ta ƙara da cewa ɗaruruwan ƙauyuka sun fuskanci hare-hare tare da tilasta wa mazauna barin gidajensu a jihohin Benue, Borno, Katsina, Sokoto, Plateau da Zamfara.

Gwamnatin Tinubu za ta dawo da binciken mai a Arewa bayan tsaida aikin tun bayan hawansa mulki 

Shugaban RMAFC ya kuma ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na damuwa da yadda aikin ya tsaya, yana mai cewa an ba gwamnonin Bauchi da Gombe tabbacin cewa za a sake tura kayan aiki da ma'aikata domin ci gaba da aikin.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img