Gwamnan Kaduna ya ce jihar na biyan N6.7bn na bashin da ta gada
Daga Wakiliya
Gwamnan Kaduna, Sanata Uba Sani, ya ce gwamnatin jihar na biyan Naira biliyan 6.7 a matsayin bashin da ta gada, wanda ya ce za a ci gaba da biya har zuwa shekarar 2048.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wata hira da shirin One-on-One na Channels Television.
Sanata Uba Sani ya ce bai cika son yawan fitowa yana surutai ba amma bashin wani bangare ne na rancen da ya gada daga gwamnatin da ta gabata, wanda ake ci gaba da biyan sa daga kudaden da jihar ke samu ta hanyar rabon kudaden tarayya na FAAC.
Ya kuma ce tun bayan da ya zama gwamnan Kaduna, bai karɓi wani sabon bashi ba.
“Muna biyan Naira biliyan 6.7 daga bashin da muka gada, kuma za mu ci gaba da biyan sa har zuwa 2048. Tun lokacin da na zama gwamna, ban ciwo ko sisi na sabon bashi ba,” in ji Sanata Uba Sani.
Gwamnan ya ce matakin na daga cikin kokarin gwamnatinsa na tabbatar da cewa jihar ba ta kara shiga wani sabon nauyin bashi ba.




