Gwamnatin Tinubu za ta dawo da binciken mai a Arewa bayan tsaida aikin tun bayan hawansa mulki
Daga Wakiliya
Gwamnatin Tarayya ta fara shirye-shiryen farfaɗo da aikin binciken man fetur a filin Kolmani da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe, bayan aikin ya tsaya.
Shugaban Hukumar Rabon Asusun Tarayya da Hukumar Kula da Kasafin Kuɗi ta Jihohi (RMAFC), Muhammad Bello, ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin ziyarar tantance aikin a Bauchi.
Muhammad Bello ya ce farfaɗo da aikin na da muhimmanci ga ci gaban Arewa maso Gabas da kuma tattalin arzikin Najeriya.
Ya ce RMAFC za ta duba matakan da suka dace domin dawo da aikin, tare da miƙa rahoton bincikenta ga hukumomin da abin ya shafa.
Shugaban RMAFC ya kuma ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na damuwa da yadda aikin ya tsaya, yana mai cewa an ba gwamnonin Bauchi da Gombe tabbacin cewa za a sake tura kayan aiki da ma'aikata domin ci gaba da aikin.
A nasa bangaren, Kwamishinan Albarkatun Ƙasa na Jihar Bauchi, Maiwada Bello, ya ce aikin binciken ya tsaya ne kusan watan Yulin 2025, bayan al'ummar yankin suka lura cewa kamfanin da ke gudanar da aikin ya fara kwashe kayansa.
Ya ce gwamnatin jihar Bauchi a ƙarƙashin Gwamna Bala Mohammed a shirye take ta samar da ma'aikata da sauran tallafin da ake bukata domin ganin an dawo da aikin.
Muhammad Bello ya kuma ziyarci Kwalejin Mai da Iskar Gas ta Bauchi, inda ya yaba wa gwamnatin jihar kan kafa cibiyar horas da ma'aikata da za su iya taka muhimmiyar rawa idan aikin Kolmani ya koma cikakken aiki.




