Labarai

Allah da ya ɗauki ran Abacha kafin zaɓe yana kallon ka – Dino Melaye ya gargadi Tinubu kan zaɓen 2027

A cewarsa, akwai abin da ya kira "ikon Allah a cikin al'amuran ɗan Adam", yana mai cewa babu wani shiri na siyasa da zai iya rinjayar nufin Allah.

Anyi wa Zenith Bank Kutse an Kwashi Bayanan Kwastomomin Bankin

Zenith Bank ta bayyana cewa bayanan da aka samu damar shiga sun haɗa da wasu adireshoshin imel (email) da kuma lambobin waya na wasu kwastomomi. Sai dai bankin ya ce har yanzu binciken yana gudana.

Ko ɗana ne ku ka kama, kada ku tausaya masa” – Gwamna Bala ya umarci jami’an tsaro su murƙushe masu haƙar ma’adinai a Bauchi...

"Ina so ku ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri. Kada ku tausaya wa kowa. Ko da ɗana ne yake da hannu a haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba, ku ɗauki mataki a kansa," in ji gwamnan.

EFCC ta rufe asusun gwamnatin Osun kwanaki 10 kafin zaɓen gwamna

Matakin ya zo ne sa'o'i kaɗan bayan Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya zargi EFCC da shirin daskarar da asusun gwamnatin jihar da kuma na wasu manyan jami'an gwamnati gabanin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar 15 ga Agusta

Sarkin Yarabawa a Legas ya gana da Hausawan Arewa mazauna Legas, ya bukace su su mallaki PVC domin mara wa Tinubu baya a 2027

Oba Ogunronbi ya yi wannan kira ne yayin da ya karɓi Sarkin Hausawan Shasha, Alhaji Ilyasu Isah Kira, da shugabannin al'ummar Hausawa daga ƙananan hukumomi shida na Alimosho a fadarsa.

Fiye da Mutum 1,000 Sun Amfana da Tallafin miliyan ɗai-dai da Kayan Sana’o’i a Lagos

Tallafin ya haɗa da kuɗi, injinan ɗinki, firiza, injinan niƙa, injinan yin abin sha, murhun gas, tare da kayan abinci kamar shinkafa, doya, ƙwai da taliyar noodles.

Zaɓen 2027: “A Ganinmu Tinubu Ya Gaza” — Ƙungiyar Igbo Ta Yi Watsi Da Ikirarin Uzodimma Da Umahi Na Goyon Bayan Tinubu a Kudu...

Ƙungiyar ta kuma buƙaci jami'an gwamnati daga Kudu maso Gabas su mayar da hankali kan ayyukan da kundin tsarin mulki ya ɗora musu da kuma magance matsalolin tattalin arzikin al'umma, maimakon yin magana a madadin dukkan 'yan Igbo kan batutuwan siyasa.

Zaɓen 2027 ya riga ya ƙare – Uba Sani ya yi wa Tinubu alƙawarin kashi 95% na ƙuri’un Kaduna

A cewarsa, ya taɓa bayyana hakan watanni biyu da suka gabata kuma har yanzu babu wanda ya kawo hujjar da ta karyata ikirarinsa.

Sojin Ruwa da Kwastam Sun Kama Buhunan Shinkafa 518 da Ake Zargin An Shigo da Su Ba Bisa Ka’ida Ba

Rundunar Sojin Ruwan ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro wajen yaki da fasa-kauri da sauran ayyukan haramtattu a yankunan ruwan kasar.

Zaɓen 2027: Sarakuna a Kwara Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga APC, Za Su Taya Jam’iyyar Yaƙin Neman Zaɓe

Shi ma Olofa na Offa, Oba Mufutau Gbadamosi Esuwye, ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa 'yan takarar APC a jihar Kwara za su samu nasara a zaɓen 2027.
- Advertisement -spot_img

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img