Fiye da Mutum 1,000 Sun Amfana da Tallafin miliyan ɗai-dai da Kayan Sana’o’i a Lagos

Fiye da Mutum 1,000 Sun Amfana da Tallafin Naira miliyan ɗai-dai da Kayan Sana’o’i a Lagos

Daga Wakiliya

Fiye da mutum 1,000 mazauna ƙaramar hukumar Lagos Mainland sun amfana da tallafin kuɗi, kayan sana’a da kayan abinci yayin bikin cika shekara guda da hawan gwamnatin shugaban ƙaramar hukumar, Jibril Emilagba.

 

Tallafin ya haɗa da kuɗi, injinan ɗinki, firiza, injinan niƙa, injinan yin abin sha, murhun gas, tare da kayan abinci kamar shinkafa, doya, ƙwai da taliyar noodles.

 

Jibril Emilagba ya ce shirin na da nufin inganta rayuwar al’umma, tallafa wa ƙananan ‘yan kasuwa da rage radadin matsin tattalin arziki. Ya ce gwamnatinsa ta ci gaba da cika alkawuran da ta ɗauka tun bayan fara aiki.

 

A cewarsa, cikin shekara guda gwamnatin ƙaramar hukumar ta raba Naira miliyan 130 ga masu sana’o’i, ‘yan kasuwa da masu ƙananan harkokin kasuwanci, tare da gudanar da shirye-shiryen tallafa wa mabukata da kayan abinci.

 

Ya bayyana cewa an gudanar da matakai goma na shirin “Ounje Emi”, an kuma raba kayan abinci a lokutan Ramadan, Azumi da Eid-el-Kabir, baya ga tallafa wa zawarawa.

 

Shugaban ƙaramar hukumar ya kuma lissafa ayyukan ci gaba da suka haɗa da gyaran titin Jebba–Tapa–Oko Baba da magudanan ruwa, gyaran makarantar firamare ta U.N.A., gyaran magudanan ruwa a Freeman Road, gyaran makarantar Kadara Primary School, gyaran manyan bututun ruwa a Ebute Metta East da kuma girka fitilun hasken rana guda 410 a ƙarƙashin shirin Light Up Lagos Mainland.

 

Haka kuma ya ce an gyara sakatariyar ƙaramar hukumar, an sayo motocin aiki ga kansiloli, ma’aikata da ƙungiyoyin kasuwanni, tare da kula da hanyoyi da dama a faɗin ƙaramar hukumar.

 

Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Abibat Bamgboye, ta yaba da wannan mataki, tana mai cewa irin wannan tallafi bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙaramar hukumar, tare da fatan sauran ƙananan hukumomi za su kwaikwayi wannan tsari domin ƙarin jama’a su amfana.

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Nigeria ta ƙaddamar da dandalin rajistar haihuwa da mutuwa ta yanar gizo

Gwamnatin ta ce samun ingantacciyar shaidar zama ɗan ƙasa na taimakawa wajen samun damar kiwon lafiya, ilimi, fasfo, ayyukan kuɗi da sauran shirye-shiryen gwamnati.

Sarkin Yarabawa a Legas ya gana da Hausawan Arewa mazauna Legas, ya bukace su su mallaki PVC domin mara wa Tinubu baya a 2027

Oba Ogunronbi ya yi wannan kira ne yayin da ya karɓi Sarkin Hausawan Shasha, Alhaji Ilyasu Isah Kira, da shugabannin al'ummar Hausawa daga ƙananan hukumomi shida na Alimosho a fadarsa.

Tinubu ya amince da ƙarin albashi ga jami’an sojin Najeriya, wasu kashi 30, wasu 50 wasu 80

Tinubu ya kuma buƙaci jami'an sojin su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alama ta godiyar gwamnati bisa hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana fatan cewa tare za su yi nasara a kan masu neman tayar da zaune tsaye a Najeriya.

Zaɓen 2027: “A Ganinmu Tinubu Ya Gaza” — Ƙungiyar Igbo Ta Yi Watsi Da Ikirarin Uzodimma Da Umahi Na Goyon Bayan Tinubu a Kudu...

Ƙungiyar ta kuma buƙaci jami'an gwamnati daga Kudu maso Gabas su mayar da hankali kan ayyukan da kundin tsarin mulki ya ɗora musu da kuma magance matsalolin tattalin arzikin al'umma, maimakon yin magana a madadin dukkan 'yan Igbo kan batutuwan siyasa.

Zaɓen 2027 ya riga ya ƙare – Uba Sani ya yi wa Tinubu alƙawarin kashi 95% na ƙuri’un Kaduna

A cewarsa, ya taɓa bayyana hakan watanni biyu da suka gabata kuma har yanzu babu wanda ya kawo hujjar da ta karyata ikirarinsa.

Kanun Labarai

Gwamnatin Nigeria ta ƙaddamar da dandalin rajistar haihuwa da mutuwa ta yanar gizo

Gwamnatin ta ce samun ingantacciyar shaidar zama ɗan ƙasa na taimakawa wajen samun damar kiwon lafiya, ilimi, fasfo, ayyukan kuɗi da sauran shirye-shiryen gwamnati.

Sarkin Yarabawa a Legas ya gana da Hausawan Arewa mazauna Legas, ya bukace su su mallaki PVC domin mara wa Tinubu baya a 2027

Oba Ogunronbi ya yi wannan kira ne yayin da ya karɓi Sarkin Hausawan Shasha, Alhaji Ilyasu Isah Kira, da shugabannin al'ummar Hausawa daga ƙananan hukumomi shida na Alimosho a fadarsa.

Tinubu ya amince da ƙarin albashi ga jami’an sojin Najeriya, wasu kashi 30, wasu 50 wasu 80

Tinubu ya kuma buƙaci jami'an sojin su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alama ta godiyar gwamnati bisa hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana fatan cewa tare za su yi nasara a kan masu neman tayar da zaune tsaye a Najeriya.

Zaɓen 2027: “A Ganinmu Tinubu Ya Gaza” — Ƙungiyar Igbo Ta Yi Watsi Da Ikirarin Uzodimma Da Umahi Na Goyon Bayan Tinubu a Kudu...

Ƙungiyar ta kuma buƙaci jami'an gwamnati daga Kudu maso Gabas su mayar da hankali kan ayyukan da kundin tsarin mulki ya ɗora musu da kuma magance matsalolin tattalin arzikin al'umma, maimakon yin magana a madadin dukkan 'yan Igbo kan batutuwan siyasa.

Zaɓen 2027 ya riga ya ƙare – Uba Sani ya yi wa Tinubu alƙawarin kashi 95% na ƙuri’un Kaduna

A cewarsa, ya taɓa bayyana hakan watanni biyu da suka gabata kuma har yanzu babu wanda ya kawo hujjar da ta karyata ikirarinsa.

Sojin Ruwa da Kwastam Sun Kama Buhunan Shinkafa 518 da Ake Zargin An Shigo da Su Ba Bisa Ka’ida Ba

Rundunar Sojin Ruwan ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro wajen yaki da fasa-kauri da sauran ayyukan haramtattu a yankunan ruwan kasar.

Zaɓen 2027: Sarakuna a Kwara Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga APC, Za Su Taya Jam’iyyar Yaƙin Neman Zaɓe

Shi ma Olofa na Offa, Oba Mufutau Gbadamosi Esuwye, ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa 'yan takarar APC a jihar Kwara za su samu nasara a zaɓen 2027.

Ku Rika Zuwa Filin Jirgin Sama Aƙalla Sa’o’i Uku Kafin Tashin Jirginku – NCAA Ta Gargadi Matafiya

Ya kuma buƙaci fasinjoji da su yi amfani da tsarin rajista ta intanet (online check-in) idan hakan ya yiwu, tare da zaɓen kujerarsu tun kafin isa filin jirgin.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img