Daga Wakiliya
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya umarci jami’an tsaro su tsaurara mataki kan masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a faɗin jihar, yana mai cewa kada a nuna wa kowa wata alfarma idan aka same shi da hannu.
Yayin da yake karɓar bakuncin sabon Babban Kwamandan Runduna ta 3 ta Sojojin Najeriya kuma Kwamandan Operation Enduring Peace, Manjo Janar Maxwell Dangana, a Fadar Gwamnatin Bauchi ranar Laraba, gwamnan ya ce haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa matsalar tsaro a jihar.
Bala Mohammed ya buƙaci jami’an tsaro su ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma kamo duk masu hannu a wannan aiki ba tare da la’akari da matsayinsu ba.
“Ina so ku ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri. Kada ku tausaya wa kowa. Ko da ɗana ne yake da hannu a haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, ku ɗauki mataki a kansa,” in ji gwamnan.
Ya kuma yi zargin cewa wasu masu faɗa a ji da masu ruwa da tsaki na cin moriyar haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba saboda ribar da ake samu daga harkar, lamarin da ya ce na ci gaba da kawo cikas ga ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya a wasu sassan jihar.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa hukumomin tsaro, yana mai bayyana cewa za a yi amfani da wani ɓangare na kuɗin tallafin tsaro na naira biliyan uku da Gwamnatin Tarayya ta bai wa jihohi wajen sayen motocin aiki domin ƙarfafa ayyukan tsaro.
Da yake mayar da martani, Gwamna Bala Mohammed ya ce an riga an bayar da kwangilar gina hanyar zuwa garin Mansur, yana mai bayyana fatan cewa aikin zai sauƙaƙa zirga-zirga tare da inganta ayyukan tsaro.
Haka kuma ya buƙaci Rundunar Sojin Najeriya ta kafa ƙarin sansanonin soja a wasu muhimman yankuna da suka haɗa da Azare da Tafawa Balewa domin ƙarfafa tsaro da inganta saurin mayar da martani ga barazanar tsaro.




