Daga Wakiliya
Tsohon Sanatan Kogi ta Yamma, Dino Melaye, ya gargadi Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya ɗauki zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027 da wasa, yana mai cewa amincewar jam'iyyun siyasa kaɗai ba ta isa ta tabbatar da makomar kowane ɗan siyasa ba.
Melaye, wanda jigo ne a jam'iyyar ADC, ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na 𝕏 a ranar Laraba.
Ya tuna da marigayi tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Sani Abacha, yana cewa a lokacin rayuwarsa jiga-jigan jam'iyyun siyasa biyar da ke tashe a wancan lokaci sun amince da shi a matsayin ɗan takararsu na shugaban ƙasa.
Sai dai Melaye ya ce duk da hakan, Abacha ya rasu a shekarar 1998 kafin ya cika burinsa na komawa shugaban ƙasa ta hanyar zaɓe (farar hula).
A cewarsa, akwai abin da ya kira “ikon Allah a cikin al'amuran ɗan Adam”, yana mai cewa babu wani shiri na siyasa da zai iya rinjayar nufin Allah.
“Allah da ya kira (dauki ran) Abacha bai tafi omugwo ba. Tinubu ya kula,” in ji Melaye.
Kalmar “omugwo” kalma ce ta al'adar kabilar Igbo, wadda ke nufin lokacin da uwa ko suruka ke kula da mace bayan ta haihu.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Shugaba Bola Tinubu ko Fadar Shugaban Ƙasa ba su fitar da wata sanarwa kan kalaman Dino Melaye ba.




