Daga Wakiliya
Majalisar Sarakunan Gargajiyar Kudancin Jihar Kwara ta bayyana cikakken goyon bayanta ga jam’iyyar APC, tare da alƙawarin wayar da kan al’umma domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a zaɓen shekarar 2027.
Sarakunan sun ce sun ɗauki wannan matsaya ne saboda abin da suka bayyana a matsayin kyakkyawan aiki da ci gaban da Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya kawo a jihar, musamman a yankin Kudancin Kwara.
Da yake jawabi a madadin sarakunan yankunan Igbomina, Ibolo da Ekiti, Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahya Alebiosu, ya ce Majalisar Sarakunan Kudancin Kwara ta amince da goyon bayan ɗan takarar gwamna na APC daga Kwara ta Arewa, Yakubu Salihu, saboda tabbatar da adalci da daidaito.
Oba Alebiosu ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamna AbdulRazaq bisa amincewa da buƙatar da aka gabatar na bai wa Kwara ta Arewa damar fitar da gwamna na gaba, yayin da yankin Igbomina zai fitar da ɗan takarar Sanatan Kudancin Kwara.
Sarkin ya kuma yi alƙawarin cewa dukkan sarakunan gargajiya na Kudancin Kwara za su ba APC cikakken goyon baya tare da yin duk abin da doka ta amince da shi domin jam’iyyar ta yi nasara a zaɓen 2027.
Hakazalika, Elerin na Erin-Ile, Oba Jimoh Adebowale Adesoye, ta bakin Onipe na Ipee, Oba Muftau Adebayo Lawal Titiloye III, ya ce al’ummar yankin Oyun za su mara wa APC baya saboda irin ayyukan ci gaban da gwamnatin AbdulRazaq ta gudanar.
Shi ma Olofa na Offa, Oba Mufutau Gbadamosi Esuwye, ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa ‘yan takarar APC a jihar Kwara za su samu nasara a zaɓen 2027.
A nasa jawabin, Shugaban APC na Jihar Kwara, Prince Sunday Fagbemi, ya gode wa sarakunan gargajiya da al’ummar yankunan Oyun, Offa da Irepodun bisa goyon bayan da suka nuna ga jam’iyyar da kuma yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani cikin lumana.




