Labarai

Kotu a Rasha Ta Kwace Kadarori 123 Mallakin Ƙungiyar Kiristoci ta Jehovah’s Witnesses

Sai dai a shekarar 2022, Kotun Kare Haƙƙin Bil Adama ta Turai ta yanke hukuncin cewa haramta ƙungiyar ya saɓa wa doka.

Biza Da Fasfo: Amurka Ta Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Amfani da Hotunan Fasfo da AI Ta Gyara

Sanarwar ta ce kada masu neman biza ko fasfo su yi amfani da AI, filtoci (filters), ko wani nau'in gyaran hoto na dijital yayin ɗaukar hoton fasfo.

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus Ko Ta Tsige Shi

Kungiyar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) Ta Bukaci Shugaban FIFA, Gianni Infantino Ya Yi Murabus, Akwai Shakku A Shugabancinsa

Barayi Sun Kutsa Makarantar Gwamnati a Jigawa Sun Yi Wa Masu Gadi Duka Sun Sace Kayan Wutan Lantarkin Makarantar

Hakazalika, ya buƙaci masu gadi da jami'an tsaro da ke kula da makarantu da sauran cibiyoyin gwamnati su ƙara sanya ido, sannan ya yi kira ga al'umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile ayyukan ɓarna a jihar.

Remi Tinubu Ta Shawarci Matasan Najeriya Su Koyi Wadatar Zuci, Su Guji Kwaɗayi da Maular Abin Hannun Wasu

"Ku koyi gamsuwa da abin da kuke da shi, kada ku zama masu kwaɗayi ko roƙon abin hannun wasu," in ji ta.

Gwamnatin Abia Ta Sanya Harajin Naira miliyan 200 da Miliyan 150 Ga Duk Dan takarar Shugaban Ƙasa da Gwamna Dake Son Saka Allon...

Gwamnatin Abia Ta Sanya Kuɗin Lasisin Allon Yaƙin Neman Zaɓe: Naira Miliyan 200 ga Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa, Miliyan 150 ga Na Gwamna Daga Wakiliya Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa duk ɗan takarar shugaban ƙasa da ke son kafa allunan yaƙin neman zaɓe (billboards) da fastoci a jihar zai biya Naira miliyan 200 domin samun lasisin yin hakan. Hukumar Kula da Allunan Talla da Alamomin Kasuwanci ta Jihar Abia (ABSSAA) ce ta bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a birnin Aba. Shugaban Sashen Dabaru, Ƙirkire-ƙirkire da Tsara na hukumar, Ndubuisi Nwaogwugwu, ya ce jadawalin kuɗaɗen ya shafi dukkan 'yan takara a matakai daban-daban. A cewarsa, ɗan takarar gwamna zai biya Naira miliyan 150, ɗan takarar Sanata Naira miliyan 100, ɗan takarar Majalisar Wakilai Naira miliyan 50, yayin da ɗan takarar Majalisar Dokokin Jiha zai biya Naira miliyan 20. Darakta Janar na Ofishin Sadarwa na Gwamnatin Abia, Onyebuchi Ememanka, ya ce tsarin ba abin cece-kuce ba ne, yana mai cewa manufarsa ita ce tabbatar da tsaro, tsaftar muhalli da kuma gudanar da yaƙin neman zaɓe cikin tsari. Ya kuma jaddada cewa gwamnati ba za ta nuna bambanci ga kowace jam'iyya ko ɗan takara ba, muddin an bi ƙa'idoji kuma an biya kuɗin da aka tanada. Sai dai Ƙungiyar Masu Tallace-tallace ta Waje ta Najeriya (OAAN) ta nuna damuwa kan sabon jadawalin kuɗin, tana mai cewa kuɗaɗen sun yi tsauri kuma za su iya kawo cikas ga tallan siyasa a jihar. Shi ma shugaban jam'iyyar ADC a Abia, Kalu Kalu, ya ce idan dokar jihar ta tanadi irin waɗannan kuɗaɗe jam'iyyarsa za ta biya. Amma idan ba haka ba ne, ya kamata a soke tsarin. Ya kuma yi nuni da cewa hukuncin Kotun Ƙoli ya bai wa ƙananan hukumomi ikon karɓar irin waɗannan kuɗaɗe, yana mai gargadin cewa duk wata doka da ta saɓa wa Dokar Zaɓe ba za ta dore ba.

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani – Sarkin Musulmi

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani - Sarkin Musulmi ya yi gargaɗi

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Yana Da Ƙwarinsa — Shugaban APC, Yilwatda

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Da Kwarainsa - inji Shugaban APC Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda
- Advertisement -spot_img

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img