Barayi Sun Kutsa Makarantar Gwamnati a Jigawa Sun Yi Wa Masu Gadi Duka Sun Sace Kayan Wutan Lantarkin Makarantar
Daga Wakiliya
Wasu da ake zargin ɓarayi ne sun kutsa cikin Makarantar Government Unity School da ke Ringim a Jihar Jigawa, inda suka yi wa masu gadin makarantar duka tare da sace mita 12 na kebul mai sulke (armoured cable) da ke haɗe da tiransifomar makarantar.
Mai magana da yawun Hukumar NSCDC ta Jihar Jigawa, ASC Badruddeen Tijjani, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 2:00 na dare ranar Alhamis, 30 ga Yuli, 2026, lokacin da sama da mutum 10 suka mamaye makarantar, suka yi galaba kan masu gadin guda uku kafin su yanke kebul ɗin suka tsere.
Ya bayyana cewa darajar kebul ɗin da aka sace na tsakanin Naira 900,000 zuwa miliyan 1.05, lamarin da ya jefa makarantar cikin duhu.
Tijjani ya ce jami’an NSCDC na shiyyar Ringim sun isa wurin bayan samun kiran gaggawa, inda suka tattara wasu shaidu da za su taimaka wajen gano waɗanda suka aikata laifin.
A nasa martanin, Kwamandan NSCDC na Jihar Jigawa, CC Muhammad Ingawa, ya yi Allah wadai da harin, yana mai bayyana shi a matsayin hari kan muhimman kadarorin gwamnati.
Ya umarci jami’ansa su ƙaddamar da farautar waɗanda ake zargi, tare da tabbatar da cewa duk wanda aka samu da hannu za a gurfanar da shi a gaban kotu.
Hakazalika, ya buƙaci masu gadi da jami’an tsaro da ke kula da makarantu da sauran cibiyoyin gwamnati su ƙara sanya ido, sannan ya yi kira ga al’umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile ayyukan ɓarna a jihar.





