Remi Tinubu Ta Shawarci Matasa Su Guji Kwaɗayi, Su Koyi Gamsuwa da Abin da Suke da Shi
Daga Wakiliya
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta buƙaci matasan Najeriya su kasance masu himma da haƙuri wajen neman nasara, tare da gargadin su da kada su zama masu kwaɗayi ko kuma su riƙa son samun komai cikin gaggawa.
Ta bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ta karɓi shugabannin reshen matasa na jam’iyyar APC a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. A taron, ta kuma ba shugabannin matasan motocin bas guda tara domin tallafa musu wajen gudanar da ayyukansu.
A cewar sanarwar da Babbar Mataimakiyarta kan Yaɗa Labarai, Busola Kukoyi, ta fitar, Oluremi Tinubu ta ƙarfafa wa matasan gwiwa da su rungumi jajircewa, haƙuri, gaskiya da aiki tukuru a matsayin ginshiƙan samun ci gaba.
Ta ce Allah ne ya fi sanin abin da kowane mutum yake buƙata, amma da yawa daga cikin matasa na son samun nasara cikin sauri ba tare da sun jira lokacin da ya dace ba.
“Ku koyi gamsuwa da abin da kuke da shi, kada ku zama masu kwaɗayi ko roƙon abin hannun wasu,” in ji ta.
Uwargidan Shugaban Ƙasar ta kuma yi wa matasan misali da gaggafa, tana mai cewa idan gaggafa ta ga hadari ba ta tsorata, sai dai ta yi amfani da iska ta tashi sama da shi.
Ta ce matasa su kasance masu neman hanyarsu ta ci gaba, maimakon kwaikwayon rayuwar wasu ko son mallakar abin da suke da shi.
Har ila yau, Sanata Oluremi Tinubu ta yaba wa shugabannin matasan APC bisa haɗin kai da suke nunawa wajen ƙarfafa jam’iyyar, musamman a matakin ƙasa, tare da ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da bayyana nasarorin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da manufofin Renewed Hope Agenda.
A ƙarshe, ta miƙa motocin bas guda tara ga Shugaban Matasan APC na Ƙasa, Mataimakinsa, shugabannin shiyyoyi da kuma shugabannin matasan jam’iyyar na Babban Birnin Tarayya (FCT), domin amfani da su wajen ayyukan jam’iyya da hidimar al’umma.




