A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi: Kada A Yi Wa Fulani Duka Laifin Ƴan Ta’adda

Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya bukaci ‘yan Najeriya da su daina kiran masu garkuwa da mutane, ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda da sunan Fulani makiyaya, yana mai cewa duk wanda ya aikata laifi a kira shi mai laifi, ba tare da danganta shi da wata ƙabila ba.

Sarkin Musulmin ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin buɗe taron ƙasa na shekarar 2026 na Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da aka gudanar a Abuja.

Ya ce bai kamata a hukunta ko a ɗora wa miliyoyin Fulani masu zaman lafiya laifin wasu tsirarun masu aikata laifuka ba.

“Ku kira su masu laifi kawai. A kowace iyali akwai nagari kuma akwai marasa kyau. Ni ina cikin iyalan nagari,” in ji Sarkin Musulmin.

Muhammadu Sa’ad Abubakar III ya kuma tabbatar da cewa al’ummomin Fulani a shirye suke su yi aiki tare da gwamnatin tarayya da jami’an tsaro domin gano tare da fatattakar masu laifi daga yankunansu.

Haka kuma, ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa kafa Ma’aikatar Raya Kiwo ta Tarayya, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen bunƙasa harkar kiwo da ci gaban masana’antar dabbobi a Najeriya.

A nasa jawabin, Shugaban ƙungiyar MACBAN na ƙasa, Baba Othman Ngelzarma, ya yi Allah wadai da ta’addanci, garkuwa da mutane, fashi da makami da satar shanu, yana mai jaddada cewa bai dace a jingina laifukan wasu tsirarun mutane da wata ƙabila, addini ko sana’a ba.

Ya ce MACBAN za ta ci gaba da ƙarfafa mambobinta su bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai tare da yin watsi da duk wani nau’in aikata laifi.

DA DUMI-DUMI

Daga Alƙawarin Wa’adi Ɗaya a 1986, Yau Shekaru 40 Kenan Yoweri Museveni Yana Mulkin Uganda Ba Tare da Ya Sauka ba

Daga Alƙawarin Wa'adi Ɗaya a 1986 Zuwa Shekaru 40 Kan Mulki: Yoweri Museveni Har Yanzu Shi Ne Shugaban Uganda

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Yana Da Ƙwarinsa — Shugaban APC, Yilwatda

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Da Kwarainsa - inji Shugaban APC Yilwatda

Za A Fara Baiwa Motocin Masu Nakasa Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

Za A Fara Baiwa Motocin Mutane Masu Nakasa ko Lalura Ta Musamman Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

Kanun Labarai

Daga Alƙawarin Wa’adi Ɗaya a 1986, Yau Shekaru 40 Kenan Yoweri Museveni Yana Mulkin Uganda Ba Tare da Ya Sauka ba

Daga Alƙawarin Wa'adi Ɗaya a 1986 Zuwa Shekaru 40 Kan Mulki: Yoweri Museveni Har Yanzu Shi Ne Shugaban Uganda

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Yana Da Ƙwarinsa — Shugaban APC, Yilwatda

Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Da Kwarainsa - inji Shugaban APC Yilwatda

Za A Fara Baiwa Motocin Masu Nakasa Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

Za A Fara Baiwa Motocin Mutane Masu Nakasa ko Lalura Ta Musamman Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img