Tinubu Na Aiki Daga Safe Har Dare, Har Yanzu Yana Da Ƙwarinsa — Shugaban APC, Yilwatda

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya yi watsi da ikirarin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Peter Obi, cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gaji da jagorantar Najeriya.

Yilwatda ya bayyana haka ne yayin wata hira da ya yi a tashar Channels Television, inda ya ce Shugaba Tinubu na gudanar da ayyukansa tun daga safe har zuwa dare, kuma har yanzu yana da ƙwarin guiwar ci gaba da cika alkawuran da ya ɗauka ga ‘yan Najeriya.

Ya ce, “Ina so in tambayi Peter Obi, shin shugaban ƙasa zai shiga wasan dambe ne ko gudun mita 400? Ta yaya za a ce mutumin da ke aiki daga safe har dare ya gaji?”

Shugaban APC ya kuma ce miliyoyin ɗalibai da iyaye mata da ke cin gajiyar shirin NELFUND ba za su yi fatan Shugaba Tinubu ya sauka daga mulki ba.

A cewarsa, ayyukan manyan tituna da tashoshin jiragen ruwa da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa, ciki har da titin Lagos zuwa Calabar, da sabbin tashoshin jiragen ruwa a Calabar, Akwa Ibom, Fatakwal, Ondo da Legas, sun nuna cewa gwamnatin na ci gaba da mayar da hankali kan bunƙasa ƙasa.

Yilwatda ya kuma ce ayyukan gyaran filayen jiragen sama da ake yi a sassan ƙasar nan, ciki har da Arewa, shaida ce cewa gwamnatin Tinubu ba ta yi kasa a gwiwa ba wajen aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa.

DA DUMI-DUMI

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani – Sarkin Musulmi

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani - Sarkin Musulmi ya yi gargaɗi

Daga Alƙawarin Wa’adi Ɗaya a 1986, Yau Shekaru 40 Kenan Yoweri Museveni Yana Mulkin Uganda Ba Tare da Ya Sauka ba

Daga Alƙawarin Wa'adi Ɗaya a 1986 Zuwa Shekaru 40 Kan Mulki: Yoweri Museveni Har Yanzu Shi Ne Shugaban Uganda

Za A Fara Baiwa Motocin Masu Nakasa Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

Za A Fara Baiwa Motocin Mutane Masu Nakasa ko Lalura Ta Musamman Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

Kanun Labarai

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani – Sarkin Musulmi

A Daina Danganta Masu Garkuwa da Mutane da Ƙabilar Fulani - Sarkin Musulmi ya yi gargaɗi

Daga Alƙawarin Wa’adi Ɗaya a 1986, Yau Shekaru 40 Kenan Yoweri Museveni Yana Mulkin Uganda Ba Tare da Ya Sauka ba

Daga Alƙawarin Wa'adi Ɗaya a 1986 Zuwa Shekaru 40 Kan Mulki: Yoweri Museveni Har Yanzu Shi Ne Shugaban Uganda

Za A Fara Baiwa Motocin Masu Nakasa Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

Za A Fara Baiwa Motocin Mutane Masu Nakasa ko Lalura Ta Musamman Lambobin Mota Na Musamman A Lagos

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img