APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila – Nentawe Yilwatda
Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa jam’iyyar za ta yi amfani da dukkan ƙarfinta na siyasa domin tabbatar da nasara a zaɓukan shekarar 2027 daga matakin kansila har zuwa kujerar shugaban ƙasa.
Yilwatda ya ce zaɓen gwamnan jihar Osun da za a gudanar a ranar 15 ga Agusta, 2026, zai zama gwajin ƙarfin jam’iyyar da kuma shirin tunkarar babban zaɓen 2027. Ya jaddada cewa lashe zaɓen Osun wajibi ne ga APC.
A cewarsa, APC tana da ƙarfin shugabanci, tsari da kuma damar lashe zaɓe a dukkan matakai, tare da bayyana cewa za a tattara gwamnoni, ‘yan majalisu da sauran shugabannin jam’iyyar domin gudanar da kamfen daga gida zuwa gida a faɗin jihar Osun.
Ya kuma yi kira ga kwamitin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar da ya haɗa kai wajen tara albarkatu, wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a da kuma tabbatar da nasarar ɗan takarar APC a jihar.
A nasa jawabin, shugaban kwamitin yaƙin neman zaɓen APC kuma gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya ce jam’iyyar za ta gudanar da kamfen cikin lumana ba tare da tashin hankali ba, tare da tabbatar da cewa za ta dawo da jihar Osun ƙarƙashin ikon APC.
Uzodimma ya ce APC za ta mayar da hankali wajen tattaunawa da al’umma, ma’aikata, manoma, ‘yan kasuwa, matasa, sarakuna da shugabannin addini, yana mai cewa jam’iyyar ba za ta bari zarge-zarge ko yaɗa bayanan ƙarya daga adawa su karkatar da hankalinta ba.
Taron ƙaddamar da kwamitin ya samu halartar gwamnonin jihohin Ekiti, Yobe, Jigawa da Kano, tare da sauran manyan jiga-jigan jam’iyyar APC.




