Labarai

Matatun man fetur din Najeriya za su dawo aiki – Tinubu

“Na karbi dukkan nauyin da ya shafi abin da ya faru a baya. Nauyin da ke kaina yanzu shi ne gyara tattalin arziki domin amfanin mafi yawan ‘yan Najeriya,” in ji shugaban.

Dan siyasar da ya rantse da Alƙur’ani zai ci gaba da biyayya ga Kwankwaso ya koma APC

Ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon abin da ya kira rashin cika alkawura daga jam’iyyar, yana mai cewa yanzu zai mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaɓen 2027 a ƙarƙashin APC.

Musulmi da Kiristoci sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Abuja

Sun kuma jaddada cewa manufar yarjejeniyar ba wai hada addinai wuri daya ba ce, sai dai gina fahimtar juna da girmama bambance-bambance.

Ana tsare da El-Rufai ne saboda ya raba gari da Tinubu – Mataimakin Atiku – M/Atiku

Ya ce, “Wace irin shaida ake bukata don tabbatar da cewa ana yakar ‘yan adawa ne ba cin hanci da rashawa ba?”

Sama da masana magunguna 9,500 suk bar Najeriya cikin shekaru biyu saboda ƙarancin albashi da kuma rashin kyawun yanayin aiki -ACPN

Sama da masana magunguna 9,500 suk bar Najeriya cikin shekaru biyu saboda ƙarancin albashi da kuma rashin kyawun yanayin aiki -ACPN

Abin da Rarara ya yi wa Pantami ‘Somin taɓi ne’ a siyasa – Rabiu Kwankwaso

Abin da Rarara ya yi wa Pantami ‘Somin taɓi ne’ ai da zarar ka bar wa’azin addini ka shiga siyasa, bai kamata ka sa ran ’yan siyasa za su ci gaba da kallonka a matsayin malamin addini ba,” in ji Rabiu Kwankwaso

An sauya jirgin Trump a asirce saboda tsoron barazanar Iran

Rahoton ya ce Trump ya fito fili ya hau Air Force One, amma daga baya aka fitar da shi a asirce ta hanyar wata motar ɗaukar kayan abinci, aka kai shi wani ƙaramin jirgin soji kirar C-32A.

Muslim-Muslim: Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta nemi a kama Sheikh Jingir

Hukumar ta ce ta kalli bidiyon cikin "tsananin damuwa", tana mai cewa Sheikh Jingir ya yi kira ga tsarin siyasa da ya keɓe wasu mutane bisa addininsu, sannan ya yi amfani da kalmar "kafirai" yayin da yake kira ga magoya bayansa su mallaki katin zaɓe domin "nuna musu iyakarsu".

Gumi ya gargadi Sheikh Jingir, amma ya ce a yi wa malamin uzuri: “Ya taso ne a Plateau, jihar da ake tsananin nuna ƙiyayya...

Dr Ahmad Gumi ya ƙara da cewa ko ɓangaren adawa ma bai kamata su rika amfani da addini ba wajen harkokin siyasa inda ya wallafa bidiyon Peter Obi dan takarar Jam'iyyar NDC da aka nuna shi yana kalaman addinanci a coci.

Muslim-Muslim: Idan Tinubu ya iya karanta Suratul Fatiha daidai, zan zaɓe shi-  MC Tagwaye ya ƙalubalanci Jingir

Kalaman nasa sun zo ne a matsayin martani ga wasu kalamai da aka danganta ga Sheikh Sani Yahaya Jingir, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a kafafen sada zumunta.
- Advertisement -spot_img

DA DUMI-DUMI

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img