Muslim-Muslim: Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta nemi a kama Sheikh Jingir

Muslim-Muslim: Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta nemi a kama Sheikh Jingir

Daga Wakiliya

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta Ƙasa (NHRC) ta yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta kama tare da gurfanar da Sheikh Sani Yahaya Jingir bisa zargin yin kalaman ƙiyayya da tunzura jama'a.

Hukumar ta yi wannan kiran ne ganin yadda ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

A wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar, Chief Tony Ojukwu, SAN, ya sanya wa hannu ranar Talata, NHRC ta ce ta yi Allah-wadai da wasu kalamai da ta ce malamin ya yi a wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta ranar Lahadi.

Muslim-Muslim: Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta nemi a kama Sheikh Jingir

Daga Wakiliya

Hukumar Kare Haƙƙin Ɗan Adam ta Ƙasa (NHRC) ta yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta kama tare da gurfanar da Sheikh Sani Yahaya Jingir bisa zargin yin kalaman ƙiyayya da tunzura jama'a.

Hukumar ta yi wannan kiran ne ganin yadda ake tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

A wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar, Chief Tony Ojukwu, SAN, ya sanya wa hannu ranar Talata, NHRC ta ce ta yi Allah-wadai da wasu kalamai da ta ce malamin ya yi a wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta ranar Lahadi.

Hukumar ta ce ta kalli bidiyon cikin “tsananin damuwa”, tana mai cewa Sheikh Jingir ya yi kira ga tsarin siyasa da ya keɓe wasu mutane bisa addininsu, sannan ya yi amfani da kalmar “kafirai” yayin da yake kira ga magoya bayansa su mallaki katin zaɓe domin “nuna musu iyakarsu”.

NHRC ta bayyana cewa irin waɗannan kalamai sun saɓa wa ƙa'idojin da suka shafi daidaito, rashin nuna bambanci da zaman lafiya tsakanin al'ummar ƙasa, waɗanda kundin tsarin mulkin Najeriya da yarjejeniyoyin ƙasa da ƙasa kan haƙƙin ɗan Adam suka tanada.

Hukumar ta ce tana kallon kalaman a matsayin zage-zage na ƙiyayya da tunzura jama'a bisa addini, tana mai gargadin cewa irin waɗannan kalamai na iya haifar da rikici a lokacin da ƙasar ke shirin shiga zaɓen 2027.

NHRC ta kuma yi kira ga Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, Darakta Janar na Hukumar DSS da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kama Sheikh Jingir tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Hukumar ta bukaci malaman addini, sarakunan gargajiya da ‘yan siyasa da su guji kalaman da za su iya raba kan al'umma.

Ta kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji siyasar da ta dogara da addini ko ƙabila, su mayar da hankali wajen tantance ‘yan takara bisa cancanta, ayyukan da suka yi wa al'umma da kuma mutunta haƙƙin ɗan Adam.

NHRC ta ce bai kamata a yi wa wani sassauci ba wajen gurfanar da masu irin waɗannan kalamai, ba tare da la'akari da matsayinsu ko jam'iyyar siyasar da suke tare da ita ba.

Hukumar ta ce za ta ci gaba da sa ido kan lamarin tare da aiki da hukumomin tsaro, INEC da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa zaɓen 2027 ya gudana cikin zaman lafiya, ba tare da kalaman ƙiyayya da tashin hankali ba.

NHRC ta bayyana cewa irin waɗannan kalamai sun saɓa wa ƙa'idojin da suka shafi daidaito, rashin nuna bambanci da zaman lafiya tsakanin al'ummar ƙasa, waɗanda kundin tsarin mulkin Najeriya da yarjejeniyoyin ƙasa da ƙasa kan haƙƙin ɗan Adam suka tanada.

Hukumar ta ce tana kallon kalaman a matsayin zage-zage na ƙiyayya da tunzura jama'a bisa addini, tana mai gargadin cewa irin waɗannan kalamai na iya haifar da rikici a lokacin da ƙasar ke shirin shiga zaɓen 2027.

NHRC ta kuma yi kira ga Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, Darakta Janar na Hukumar DSS da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta kama Sheikh Jingir tare da gurfanar da shi a gaban kotu.

Hukumar ta bukaci malaman addini, sarakunan gargajiya da ‘yan siyasa da su guji kalaman da za su iya raba kan al'umma.

Ta kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji siyasar da ta dogara da addini ko ƙabila, su mayar da hankali wajen tantance ‘yan takara bisa cancanta, ayyukan da suka yi wa al'umma da kuma mutunta haƙƙin ɗan Adam.

NHRC ta ce bai kamata a yi wa wani sassauci ba wajen gurfanar da masu irin waɗannan kalamai, ba tare da la'akari da matsayinsu ko jam'iyyar siyasar da suke tare da ita ba.

Hukumar ta ce za ta ci gaba da sa ido kan lamarin tare da aiki da hukumomin tsaro, INEC da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa zaɓen 2027 ya gudana cikin zaman lafiya, ba tare da kalaman ƙiyayya da tashin hankali ba.

DA DUMI-DUMI

An sauya jirgin Trump a asirce saboda tsoron barazanar Iran

Rahoton ya ce Trump ya fito fili ya hau Air Force One, amma daga baya aka fitar da shi a asirce ta hanyar wata motar ɗaukar kayan abinci, aka kai shi wani ƙaramin jirgin soji kirar C-32A.

Gumi ya gargadi Sheikh Jingir, amma ya ce a yi wa malamin uzuri: “Ya taso ne a Plateau, jihar da ake tsananin nuna ƙiyayya...

Dr Ahmad Gumi ya ƙara da cewa ko ɓangaren adawa ma bai kamata su rika amfani da addini ba wajen harkokin siyasa inda ya wallafa bidiyon Peter Obi dan takarar Jam'iyyar NDC da aka nuna shi yana kalaman addinanci a coci.

Muslim-Muslim: Idan Tinubu ya iya karanta Suratul Fatiha daidai, zan zaɓe shi-  MC Tagwaye ya ƙalubalanci Jingir

Kalaman nasa sun zo ne a matsayin martani ga wasu kalamai da aka danganta ga Sheikh Sani Yahaya Jingir, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a kafafen sada zumunta.

Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja domin duba yiwuwar dunƙulewa su marawa mutum ɗaya a 2027

G100 ta ce ta riga ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu daga cikin manyan ‘yan siyasar adawa, ciki har da Atiku Abubakar na ADC, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso na NDC, da kuma wakilan Seyi Makinde na APM, PDP, PRP da SDP.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da ƙarin albashi ga ma’aikatan jami’o’in jihar Kano

Haka kuma, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da duba yiwuwar kafa kwamitocin ziyara (Visitation Panels) ga jami’o’in biyu da sauran manyan makarantun jihar, domin ƙara inganta sa ido, shugabanci da yadda ake tafiyar da cibiyoyin ilimi.

Kanun Labarai

An sauya jirgin Trump a asirce saboda tsoron barazanar Iran

Rahoton ya ce Trump ya fito fili ya hau Air Force One, amma daga baya aka fitar da shi a asirce ta hanyar wata motar ɗaukar kayan abinci, aka kai shi wani ƙaramin jirgin soji kirar C-32A.

Gumi ya gargadi Sheikh Jingir, amma ya ce a yi wa malamin uzuri: “Ya taso ne a Plateau, jihar da ake tsananin nuna ƙiyayya...

Dr Ahmad Gumi ya ƙara da cewa ko ɓangaren adawa ma bai kamata su rika amfani da addini ba wajen harkokin siyasa inda ya wallafa bidiyon Peter Obi dan takarar Jam'iyyar NDC da aka nuna shi yana kalaman addinanci a coci.

Muslim-Muslim: Idan Tinubu ya iya karanta Suratul Fatiha daidai, zan zaɓe shi-  MC Tagwaye ya ƙalubalanci Jingir

Kalaman nasa sun zo ne a matsayin martani ga wasu kalamai da aka danganta ga Sheikh Sani Yahaya Jingir, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a kafafen sada zumunta.

Atiku, Obi, Kwankwaso da Makinde za su gana a Abuja domin duba yiwuwar dunƙulewa su marawa mutum ɗaya a 2027

G100 ta ce ta riga ta gudanar da shawarwari na sirri da wasu daga cikin manyan ‘yan siyasar adawa, ciki har da Atiku Abubakar na ADC, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso na NDC, da kuma wakilan Seyi Makinde na APM, PDP, PRP da SDP.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da ƙarin albashi ga ma’aikatan jami’o’in jihar Kano

Haka kuma, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da duba yiwuwar kafa kwamitocin ziyara (Visitation Panels) ga jami’o’in biyu da sauran manyan makarantun jihar, domin ƙara inganta sa ido, shugabanci da yadda ake tafiyar da cibiyoyin ilimi.

Ban taɓa cin amanar matata ba tun bayan aurenmu -Aregbesola

Aregbesola ya bayyana hakan ne yayin wani gangamin ADC a Ejigbo, Jihar Osun, inda ya ce tsoron Allah da kuma sadaukarwarsa ga aurensa ne suka sa ya kasance mai aminci.

SOKOTO: An rufe makarantu a kananan hukumomi 20 saboda rashin tsaro

Shugaban kungiyar Shugabannin Makarantu ta All Nigerian Conference of Principals of Secondary Schools, Muhammad Ikililu, ya ce rashin tsaro ya dade yana kawo cikas ga tsarin makarantun kwana a jihar.

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya

Ana zargin Malam Jingir da amfani da addini wajen siyasa da rura ƙiyayya
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img