Musulmi da Kiristoci sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Abuja
Daga Wakiliya
Musulmi da Kiristoci a Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da ke neman karfafa fahimtar juna da zaman tare tsakanin bangarorin biyu.
An cimma yarjejeniyar ne a Abuja yayin wani taron kasa da kasa da kungiyoyin RABIDA da JIBWIS suka shirya, wanda ya samu halartar malaman addini daga Najeriya da kasashen waje.
Yarjejeniyar ta kunshi mutunta addinin juna, kauce wa kalaman kiyayya da kuma dakile duk wani abu da ka iya haddasa rikici.
Masu shirya taron sun ce shawarwarin da aka cimma za a mika su ga gwamnatin Najeriya domin taimakawa wajen karfafa zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kiristoci.
Sun kuma jaddada cewa manufar yarjejeniyar ba wai hada addinai wuri daya ba ce, sai dai gina fahimtar juna da girmama bambance-bambance.




