Dan siyasar da ya rantse da Alƙur’ani zai ci gaba da biyayya ga Kwankwaso ya koma APC
Daga Wakiliya
Kabiru Adamu Abdullahi, wani jigo kuma na kusa da jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya fice daga jam’iyyar NDC zuwa jam’iyyar APC mai mulki.
Abdullahi, wanda shi ne ɗan takarar mataimakin shugaban jam'iyyar NDC a baya ya yi mubaya’a ga Kwankwaso tare da yin rantsuwa da Alƙur’ani bayan rashin jituwarsa da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.
A wata wasiƙa da ya aika wa shugaban jam’iyyar NDC na Kofar Ruwa a ƙaramar hukumar Dala da ke Kano, Kabiru Adamu Abdullahi ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar nan take.
Ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon abin da ya kira rashin cika alkawura daga jam’iyyar, yana mai cewa yanzu zai mara wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu baya a zaɓen 2027 a ƙarƙashin APC.
“Ina tare da Kwankwaso tsawon shekaru 29, amma abin da na samu shi ne alkawuran da ba a cika mini su ba. Zan koma inda zan samu ƙarin daraja,” in ji Abdullahi.
Ya gode wa jam’iyyar NDC bisa damar da ta ba shi ta yi mata hidima, amma ya ce ya yanke shawarar kawo ƙarshen kasancewarsa a cikinta.




