Abin da Rarara ya yi wa Pantami ‘Somin taɓi ne’ ai da zarar ka bar wa’azin addini ka shiga siyasa, bai kamata ka sa ran ’yan siyasa za su ci gaba da kallonka a matsayin malamin addini ba,” in ji Rabiu Kwankwaso
Daga Wakiliya
Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce kalaman da mawaki Dauda Kahutu Rarara ya yi wa tsohon ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, wani ɓangare ne na abin da mutum zai fuskanta idan ya shiga siyasa.
Rabiu Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da DCL, inda ya ce Rarara ya taɓa zagin sa da kuma wasu tsoffin gwamnonin Kano, ciki har da Ibrahim Shekarau da Abdullahi Umar Ganduje.
Ya ce su a matsayinsu na ’yan siyasa sun saba fuskantar irin waɗannan kalamai, kuma sun san yadda za su tafiyar da lamarin.
“Da zarar ka bar wa’azin addini ka shiga siyasa, bai kamata ka sa ran ’yan siyasa za su ci gaba da kallonka a matsayin malamin addini ba,” in ji Rabiu Kwankwaso.
Game da rikicin da ya kunno kai tsakanin Rarara da Pantami, Rabiu Kwankwaso ya ce shi ma Pantami ya taɓa yi masa kalaman batanci a gaban magoya bayansa.
Ya ce a lokacin ne shi ya nemi magoya bayansa su kwantar da hankalinsu, duk da cewa akwai lokacin da wasu daga cikin magoya bayansa suka yi ƙoƙarin ɗaukar mataki kan Pantami saboda kalaman da ya yi masa.
Rabiu Kwankwaso ya kuma yi tsokaci kan tarihin siyasar Pantami, yana mai cewa tsohon ministan ya taɓa sukar jam’iyyar PDP tare da kiran ta da wasu kalamai masu tsauri, amma daga baya ya shiga jam’iyyar kuma ya yi takara a ƙarƙashin tutarta.
Ya ce ya kamata a yi taka-tsantsan don kada Sheikh Sani Yahaya Jingir ya tsinci kansa cikin irin wannan yanayi na sauya matsaya bayan shiga siyasa.
Kalaman Rabiu Kwankwaso sun zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan wasu kalamai da Dauda Kahutu Rarara ya yi kan Isa Ali Ibrahim Pantami.




