wakiliya

Ɗaya daga cikin jiga-jigan da suka kafa APC ya ce sun yi kuskure, ya roƙi Allah Ya yafe musu

Jalal, wanda a yanzu yake cikin jam’iyyar adawa, na daga cikin masu fafutukar adawa da gwamnatin APC a matakin jiha da tarayya, yayin da ake tunkarar zaɓen 2027 suna da burin kawar da APC daga sama har ƙasa.

Ana fargabar Amurka za ta iya kama Tinubu a Taron MDD (UNGA) – Amma Jakadan Najeriya ya ce babu abin fargaba

A wani ɓangare kuma, ya ce ba dole ba ne shugaban ƙasa ya halarci dukkan tarukan UNGA da kansa, domin ana iya tura mataimakin shugaban ƙasa ko ministan harkokin wajen ƙasa.

Ma’aikatan Gwamnati sun nemi Tinubu ya dawo da tallafin man fetur saboda tsadar rayuwa

Ma’aikatan Gwamnati sun nemi Tinubu ya dawo da tallafin man fetur saboda tsadar rayuwa Daga Wakiliya  Gamayyar Haɗakar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya sun yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta dawo da tallafin man fetur, tare da samar da wani alawus na dindindin na tsadar rayuwa (COLA) ga ma’aikatan tarayya domin rage musu radadin hauhawar farashin kayayyaki. Kiran na kunshe ne cikin wata takardar bukatu mai taken “Federal Workers Charter of Demands”, wadda mai gudanar da kungiyar, Andrew Emelieze, ya sanya wa hannu. Ma’aikatan sun kuma bukaci gwamnati ta fara biyan kashi 40 na alawus na musamman da kuma duk basussukan da suka taso tun bayan fara aiki da sabon mafi ƙarancin albashi a watan Yulin 2024. Sun kuma nemi a biya ma’aikata sauran basussukan albashi, musamman na ƙarin girma da aka samu, tare da biyan dukkan bashin fansho da wadanda suka yi ritaya suke bin gwamnati. Kungiyar ta kuma bukaci gwamnati ta samar da tsarin tallafin iyalai ga ma’aikata, inshorar lafiya ga ma’aikata da ‘yan fansho, da kuma rage harajin da ake cirewa daga alawus-alawus. Haka kuma, sun nemi gwamnati ta dauki matakan rage farashin kayan masarufi, musamman siminti, ta hanyar kara samar da kayayyakin bukatun yau da kullum a cikin gida domin samar da ayyukan yi. A bangaren jin dadin jama’a, ma’aikatan sun nemi a samar da tsarin tallafi ga marasa aikin yi da masu karamin karfi, tare da samar da kulawar lafiya kyauta ga yara, mata masu juna biyu da tsofaffi a asibitocin gwamnati. Sun kuma yi kira ga gwamnati da ta kawo karshen matsalar tsaro tare da tabbatar da sakin mutanen da aka sace a fadin kasar. Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta cire tallafin man fetur ne a ranar 29 ga Mayun 2023, lamarin da ya jawo karin farashin man fetur da kuma tashin farashin sufuri da sauran kayayyaki.

Janar Christopher Musa ya buɗe Ƙudan Zuma: Yanzu dole ya shirya buɗe kundin tarihi

Janar Martin Luther Agwai, ɗan Kudancin Kaduna kuma tsohon Babban Hafsan Sojojin Ƙasa da Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, ya yi bayani kan tarihin rikice-rikicen yankin. Akwai rikicin Kafanchan na 1987, Zangon Kataf na 1992, rikicin Shari’a na 2000 da kuma rikicin bayan zaɓen 2011.

“Ta baya yake saduwa da ni, har lokacin al’ada sai ya neme ni; ya shafa mini cututtuka, ya kwace mini fasfo, shi ya sa...

Ta bayyana cewa Gumi da matarsa ne kawai mutanen da ta sani a Najeriya ban da mijinta, don haka ta ga gidan nasu a matsayin wurin da za ta samu mafaka.

Idan lokaci ya yi, za mu sanar da ɗan takarar Shugaban Ƙasa guda da zai wakilci ƙawancen jam’iyyun adawa – Babangida Aliyu

Alhaji Babangida Aliyu ya bayyana hakan ne a Abuja yayin ƙaddamar da ofishin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar APM,

Iyalin El-Rufai sun bai wa Ministan Tsaro kwana bakwai ya janye kalamansa ko su maka shi kotu

Sun bukaci Janar Musa ya janye zargin ta kafar da ya yi amfani da ita wajen bayyana shi, inda suka ce za su dauki matakin shari’a idan bai yi hakan ba cikin kwanaki bakwai.

“APC ba ta biyan magoya baya su halarci gangami” – Bashir Ahmad

Ya ce abin da jam’iyyar ke yi shi ne samar da isasshen abinci da abin sha, tare da tabbatar da cewa an kula da magoya bayanta yadda ya kamata a lokacin gangami da sauran shirye-shiryen jam’iyyar.

Kamfanin matatar Dangote ya sanya N5,250 a matsayin mafi ƙarancin kuɗin sayen hannun jari

Dangote ya ce an tsara shirin ne domin kowa ya samu damar mallakar wani kaso a matatar, ciki har da direbobi, masu girki, ma’aikata da manajoji.

Duk Ɗan Arewa Bai Kamata Ya Ji Daɗin Kalaman Christopher Musa Ba

Duk Ɗan Arewa Mai Hankali Da Hangen Nesa Bai Kamata Ya Ji Daɗin Kalaman Ministan Tsaro Christopher Musa A Kan El-Rufa'i Ba

About Me

437 POSTS
1 COMMENTS
- Advertisement -spot_img

Latest News

Shaharata a ƙauyukan Gombe ta fi abin da ake gani a kafafen sada zumunta’ – Pantami

Ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta fi mayar da hankali kan bunƙasa ilimi, samar da ayyukan yi da koyar da matasa sana’o’in zamani, maimakon dogaro da rabon kuɗi.
- Advertisement -spot_img