Wakiliya ta ruwaito daga Jaridar The Nation cewa an dauki matakin ne bisa umarnin Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas.
Sanarwar ta ce Yilwatda zai kuma yi amfani da lokacin wajen tsara taron kwamitin gudanarwar jam’iyyar na ƙasa (NWC), wanda zai duba nasarorin da APC ta samu da kuma kalubalen da ke gabanta.
Shehu Sani ya ce a maimakon a duba yadda matsalar ta samo asali da kuma rawar da shugabannin da suka gabata suka taka wajen magance ta, ana ta ɗora alhakin matsalar kan gwamnatocin da ke kan mulki.
Ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta fi mayar da hankali kan bunƙasa ilimi, samar da ayyukan yi da koyar da matasa sana’o’in zamani, maimakon dogaro da rabon kuɗi.