Daga Wakiliya
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da yi wa ƙananan ‘yan kasuwa (MSMEs) 250,000 a faɗin Najeriya rijistar kasuwanci ta Hukumar CAC kyauta.
An sanar da hakan ne a ranar Asabar yayin bikin karrama ƙananan ‘yan kasuwa karo na 8 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
Gwamnatin Tarayya ta ce shirin zai taimaka wa ƙananan ‘yan kasuwa su yi rijistar kasuwancinsu ba tare da biyan kuɗin CAC ba, domin su samu damar cin gajiyar ayyukan bankuna da sauran shirye-shiryen gwamnati.
Baya ga rijistar kyauta, gwamnati za ta ba waɗanda suka ci gajiyar shirin horo kan yadda za su gudanar da kasuwancinsu domin ya bunƙasa.
An kuma bayyana cewa masu sha’awar cin gajiyar shirin za su shiga shafin SMEDAN domin cike bayanansu kafin a zaɓe su.
Shirin haɗin gwiwa ne tsakanin Hukumar CAC da Hukumar Bunƙasa Ƙananan da Matsakaitan Kasuwanci ta Najeriya (SMEDAN).





