Matuƙin jirgi ya kamu da farfaɗiya a sararin samaniya yana tsaka da tuka fasinjoji

Daga Wakiliya

Fasinjoji sun taimaka wajen dakile matuƙin jirgi bayan ya kamu da matsalar lafiya a sararin samaniya

Fasinjoji sun shiga tsakani domin taimakawa bayan matuƙin wani jirgin saman Air Canada ya kamu da matsalar lafiya yayin da jirgin ke tsaka da tafiya daga Newark na Amurka zuwa Halifax a ƙasar Canada.

Kamfanin Air Canada ya ce mataimakin matuƙin jirgin ne ya karɓi ragamar sarrafa jirgin tare da karkatar da shi zuwa Boston, inda aka sauka lafiya da fasinjoji 61 da ke cikinsa.

Wani fasinja, Rodney McDonald, ya ce ya fara zargin akwai matsala ne bayan jirgin ya riƙa karkacewa ba tare da alamar girgizar iska ba. Ya ce daga bisani ma’aikaciyar jirgi ta shiga ɗakin matuƙa kafin aka fito da kyaftin ɗin zuwa cikin jirgin.

McDonald ya ce shi da wasu fasinjoji sun taimaka wajen riƙe kyaftin ɗin, wanda ake zargin ya kamu da farfaɗiya, har na kusan mintuna 40 yayin da mataimakin matuƙin ke saukar da jirgin cikin aminci.

Haka kuma, wata ma’aikaciyar jinya da ke cikin jirgin ta taimaka wajen kula da lafiyar kyaftin ɗin har zuwa saukar jirgin.

An garzaya da matuƙin zuwa asibiti domin samun kulawa, yayin da Air Canada ta tabbatar da cewa an horar da matuƙan jiragen ta yadda za su iya saukar da jirgi cikin aminci ko da matuƙi ɗaya ne kawai ke aiki.

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img