Daga 1 ga Octoba WhatsApp zai fara cazar kuɗi kan saƙonnin da ake tura wa na kasuwanci

Daga 1 ga Octoba WhatsApp zai fara cazar kuɗi kan saƙonnin da ake tura wa na kasuwanci

Daga Wakiliya

Kamfanin Meta, mai WhatsApp, ya sanar da cewa daga ranar 1 ga Oktoba, 2026, zai fara karɓar kuɗi kan wasu saƙonnin da ‘yan kasuwa ke aikawa wa kwastomominsu ta manhajar WhatsApp.

 

Sabon tsarin zai shafi kamfanoni da ke amfani da WhatsApp Business Platform, wadda aka fi sani da WhatsApp Business API, wajen tura saƙonni ga dimbin kwastomomi.

 

Ba zai shafi masu amfani da WhatsApp na yau da kullum ba, kuma ba zai sanya masu amfani da manhajar WhatsApp Business ta yau da kullum su fara biyan kuɗi ba.

 

A Najeriya, rahoton ya ce saƙon da ke ƙarƙashin nau’in service/utility zai kai kusan dala $0.0101, wato kimanin Naira 14, yayin da saƙonnin talla za su fi tsada, inda za su kai kusan dala $0.062, kwatankwacin Naira 84 ga kowane saƙo.

 

Misali, idan wata kamfanin fasahar kuɗi a Najeriya ya aika saƙonni 500,000 da ake caji, zai iya kashe kusan dala $5,050 a matsayin kuɗin saƙonnin Meta kaɗai.

 

Wannan sabon tsarin na iya shafar bankuna, kamfanonin fintech, kamfanonin jiragen sama, ‘yan kasuwa, kamfanonin sadarwa da sauran ƙananan da manyan ‘yan kasuwa da ke amfani da WhatsApp wajen hulɗa da kwastomomi.

 

A halin yanzu, WhatsApp na ba wa wasu kamfanoni damar aika saƙonnin sabis kyauta cikin wa’adin sa’o’i 24 bayan kwastoma ya fara hulɗa da su.

 

Sai dai daga Oktobar 2026, za a cire wasu daga cikin wannan damar ta kyauta, lamarin da zai sa kamfanoni su riƙa biyan kuɗi gwargwadon adadin saƙonnin da suka aika.

 

Meta ta fara sauya tsarin farashin WhatsApp Business tun watan Yulin 2025, lokacin da ta sauya daga tsarin cajin kowace tattaunawa zuwa tsarin cajin kowane saƙo ga wasu saƙonnin da kamfanoni ke farawa.

 

Masana harkokin kasuwanci na ganin sabon tsarin zai iya sa ƙananan kamfanoni da sabbin ‘yan kasuwa su ƙara taka-tsantsan wajen amfani da WhatsApp wajen tallace-tallace da hulɗa da kwastomomi.

 

Farashin saƙonnin zai kuma bambanta daga ƙasa zuwa ƙasa, gwargwadon inda wanda ake aikawa wa saƙon yake da kuma nau’in saƙon.

 

Sai dai sabon tsarin ba yana nufin WhatsApp za ta fara cajin kuɗi ga talakawan da ke amfani da manhajar ba.

 

Mutanen da ke amfani da WhatsApp na yau da kullum za su ci gaba da aikawa da karɓar saƙonni ba tare da wannan sabon cajin ba.

 

Canjin ya fi shafar kasuwancin da ke amfani da WhatsApp Business Platform wajen gudanar da hulɗa da kwastomomi a babban sikeli.

DA DUMI-DUMI

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

NELFUND: Mun raba wa ɗalibai miliyan 1.2 Naira biliyan 322 -Gwamnatin Tarayya 

Shugaba Tinubu ya ce ana buƙatar NELFUND ya kasance mai isasshen kuɗi kuma mai ɗorewa domin ci gaba da biyan buƙatun ɗaliban Najeriya.

Hare-haren ’yan bindiga ya kashe mutane fiye da 10,000 cikin shekaru biyu na gwamnatin Tinubu – Amnesty

Amnesty ta ƙara da cewa ɗaruruwan ƙauyuka sun fuskanci hare-hare tare da tilasta wa mazauna barin gidajensu a jihohin Benue, Borno, Katsina, Sokoto, Plateau da Zamfara.

Gwamnatin Tinubu za ta dawo da binciken mai a Arewa bayan tsaida aikin tun bayan hawansa mulki 

Shugaban RMAFC ya kuma ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na damuwa da yadda aikin ya tsaya, yana mai cewa an ba gwamnonin Bauchi da Gombe tabbacin cewa za a sake tura kayan aiki da ma'aikata domin ci gaba da aikin.

Kanun Labarai

Shin Muna Tunanin Za Mu Yi Watsi da Almajirai Mu Samu Zaman Lafiya?

Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba? 

Dino Melaye ya shawarci Tinubu da iyalansa su fara tattara kayansu daga Villa – APC za ta sha kaye a 2027

Melaye ya ce matsalolin yunwa, kashe-kashe da sata sun nuna cewa akwai babban gibi tsakanin gwamnati da al’ummar ƙasar.

NELFUND: Mun raba wa ɗalibai miliyan 1.2 Naira biliyan 322 -Gwamnatin Tarayya 

Shugaba Tinubu ya ce ana buƙatar NELFUND ya kasance mai isasshen kuɗi kuma mai ɗorewa domin ci gaba da biyan buƙatun ɗaliban Najeriya.

Hare-haren ’yan bindiga ya kashe mutane fiye da 10,000 cikin shekaru biyu na gwamnatin Tinubu – Amnesty

Amnesty ta ƙara da cewa ɗaruruwan ƙauyuka sun fuskanci hare-hare tare da tilasta wa mazauna barin gidajensu a jihohin Benue, Borno, Katsina, Sokoto, Plateau da Zamfara.

Gwamnatin Tinubu za ta dawo da binciken mai a Arewa bayan tsaida aikin tun bayan hawansa mulki 

Shugaban RMAFC ya kuma ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu na damuwa da yadda aikin ya tsaya, yana mai cewa an ba gwamnonin Bauchi da Gombe tabbacin cewa za a sake tura kayan aiki da ma'aikata domin ci gaba da aikin.

Duk wanda ya ce bai amfana da tallafin Tinubu ba, to baya Najeriya – Gwamnan Sokoto, Ahmed Aliyu 

Gwamnan ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su sake zaben Bola Tinubu a 2027, yana mai cewa yana da yakinin shugaban zai ci gaba da kawo sauyi a kasar.

Murna Ta Koma Ciki: Tinubu ya janye sunayen kwamitin yakin neman zaɓensa na 2027 da APC ta fitar ya sa a sake gyare-gyare

Yanzu dai ana sa ran sabon jerin kwamitin zai ƙara wakiltar sassa daban-daban na jam’iyyar tare da shigar da manyan jiga-jiganta kafin fara babban yaƙin neman zaɓen 2027.

Maza ba wawaye bane: Ba za ki yi wa mijinki rashin kunya sannan ki sa ran zai ci gaba da sonki ba – Zainab

Jamiu Zainab ta ce wasu mata ba sa son a yi musu gyara, kuma kan yi gardama ko mayar da magana idan mazajensu suka yi magana da su.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img