Na Daina Zuwa Coci Domin Duk Coci da Na Je Ban Samu Natsuwa da Farin Cikin da Nake Nema Ba – AY Makun

Fitaccen ɗan wasan barkwanci kuma jarumi a Najeriya, AY Makun, ya bayyana dalilin da ya sa ya daina halartar ibadar coci, yana mai cewa hakan ba saboda ya daina imani da Allah ba ne, sai dai saboda irin yadda wasu mambobin coci suka riƙa kallonsa bayan labaransa sun bazu a kafafen sada zumunta.

AY Makun ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram, inda ya ce ya daina zuwa cocinsa na farko saboda ba ya son ya kasance abin raɗe-raɗi da kallon ban mamaki a cikin gidan ibada.

Ya ce daga baya ya fara zuwa wata sabuwar coci, inda aka tarbe shi hannu bibbiyu, har ya gana da fasto, iyalansa da wasu shugabannin cocin, lamarin da ya sa ya yi tunanin ya sami wurin ibada da zai ci gaba da zuwa.

Sai dai AY Makun ya ce bayan an gayyace shi ya shiga wani shiri a cocin, daga bisani aka sanar da shi cewa an cire sunansa saboda fargabar yadda jama’a za su ɗauki matakin idan aka haɗa shi da shirin.

Jarumin ya jaddada cewa ba ya sukar fastoci, illa dai yana son tunatar da coci rawar da ya kamata ta taka wajen karɓar mutane musamman waɗanda ke fuskantar ƙalubale ko suka shiga cece-kuce.

AY Makun ya ce ko da zarge-zargen da ake yi masa gaskiya ne ko ƙarya, coci ita ce ya kamata ta zama mafaka ta gaskiya, gafara da gyaran rayuwa.

Ya ƙara da cewa idan mutum ba zai iya komawa gidan Allah ba lokacin da yake cikin ƙunci, to hakan na nufin ya rasa wurin neman natsuwa da sabuwar dama.

DA DUMI-DUMI

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Kanun Labarai

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img