Kiristoci da masu bautar gargajiya na iya neman auren ‘yata idan suna da hali nagari – Malamin Musulunci TAOSAF
Shahararren malamin Musulunci, Taoheed Abdulwasiu Mustapha (TAOSAF), ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta bayan ya bayyana cewa Kiristoci da masu bin addinan gargajiya na iya neman auren ‘yarsa, muddin suna da kyawawan halaye kuma suna da halalacciyar hanyar samun abin rayuwa.
A cikin wani saƙo da ya wallafa, TAOSAF ya ce shi Musulmi ne, amma yana ɗora darajar ɗan Adam da mutunci a gaba.
Ya ce duk wanda ya fito daga gida nagari, yana da kyawawan ɗabi’u kuma yana da abin dogaro na halal, zai girmama shi kuma ba zai hana shi neman auren ‘yarsa ba saboda bambancin addini.
Malamin ya kuma bayyana cewa ba ya goyon bayan duk wata fahimtar addini da ke koyar da ƙiyayya ko nuna wariya ga mutane saboda bambancin addini.
Sai dai kalamansa sun haddasa muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta, inda wasu suka yaba da kiran zaman lafiya da haƙuri tsakanin mabiya addinai, yayin da wasu kuma suka nuna rashin amincewarsu da ra’ayin.
Wakiliya ta lura cewa batun ya ci gaba da jan hankalin jama’a, musamman kan batun aure tsakanin mabiya addinai daban-daban da kuma zaman tare cikin mutunta juna.





