Daga Wakiliya
Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai samu gagarumar nasara a Arewacin Najeriya a zaɓen shekarar 2027.
A wata hira da ya yi da Arise News, Uba Sani ya ce al’ummar Arewa ba za su yi zaɓe bisa addini, ƙabila ko yanki ba, sai dai bisa abin da suke ganin ya dace.
Ya kuma soki masu cewa zaɓen 2027 zai kasance tsakanin jam’iyyar APC da al’ummar Najeriya, yana mai cewa wannan hujja ce mai rauni.
“Tinubu zai yi nasara a Arewa a 2027. Mutanen Arewa ba za su yi zaɓe bisa addini, ƙabila ko yanki ba. Kuma masu cewa zaɓen zai kasance tsakanin APC da al’ummar Najeriya suna gabatar da hujja mafi rauni da na taɓa ji,” in ji shi.





