Bai kamata ana sukar bashin da Tinubu ke karbowa ba duba da amfaninsa -inji Ministan Kudi

A daina sukar bashin da Tinubu ke karbowa a  dubi abin da ake yi da kuɗin -inji Ministan Kudi

Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Tattalin Arzikin Najeriya, Taiwo Oyedele, ya ce sukar bashin da gwamnati ke ci ba tare da la’akari da dalilin aro, farashinsa da ribar da zai haifar ba, ba hanya ce mai amfani ba.

Da yake jawabi a taron Capital Market Academics of Nigeria (CMAN) a Abuja ranar Talata, Oyedele ya ce abin da ya kamata a tambaya shi ne ko an yi amfani da bashin wajen samar da ayyuka da ci gaban da zai zarce kuɗin ruwa da za a biya.

Ya ce Najeriya ta ɗauki bashi a matsayin abin kunya maimakon kayan aikin bunƙasa tattalin arziki, yana mai cewa idan aka tsara shi yadda ya dace, bashi na iya hanzarta ci gaba maimakon zama matsala.

Ministan ya kuma yi kira ga ‘yan kasuwa da su rungumi tsarin haɗa jari (equity) maimakon nacewa mallakar kashi 100 cikin 100 na ƙananan kamfanoni, yana mai cewa hakan zai ba su damar faɗaɗa kasuwancinsu.

Oyedele ya ƙara da cewa Najeriya na buƙatar inganta amincewar masu zuba jari ta hanyar tabbatar da daidaiton manufofi, kare kwangiloli da kuma kafa kotun musamman da za ta rika warware rikice-rikicen kasuwanci cikin gaggawa.

Ya kuma bayyana cewa gibin kuɗaɗen da ƙananan da matsakaitan sana’o’i (MSMEs) ke buƙata ya haura dala biliyan 200, yana mai kira da a samar da sabbin hanyoyin samun jari domin bunƙasa kasuwanci.

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img