Daga Wakiliya
Kungiyar Kwallon kafa ta Galatasaray na ƙoƙarin shawo kan ɗan wasan Najeriya, Victor Osimhen, ya ci gaba da zama a ƙungiyar, inda ake shirin ba shi fitacciyar riga mai lamba 9 da kuma mukamin kyaftin na ƙungiyar.
Osimhen dai yana sanye da riga mai lamba 45 tun bayan zuwansa daga Napoli, saboda Mauro Icardi ne ke riƙe da lamba 9. Sai dai ana sa ran Icardi zai bar ƙungiyar a ƙarshen watan Yuni, lamarin da zai ba Galatasaray damar miƙa wa Osimhen wannan muhimmiyar lamba.
Rahotanni sun ce kulob din na kallon Osimhen a matsayin jagoran ɗakin canza kaya, kuma suna ganin ba shi irin wannan matsayi zai ƙara masa ƙwarin gwiwar ci gaba da zama a Turkiyya.
Hakan na zuwa ne yayin da manyan kungiyoyi irin su Manchester United, Arsenal, Real Madrid, Barcelona, Atletico Madrid da Chelsea ke zawarcin tauraron ɗan wasan.
Osimhen ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin Galatasaray a bana, inda ya ci ƙwallaye 15 tare da bayar da taimako 5 a gasar lig, baya ga rawar da ya taka a Gasar Zakarun Turai.





