Daga Wakiliya
Jarumar fina-finan Nollywood, Halima Abubakar, ta bayyana cewa ta rungumi addinin Kiristanci bayan ta ce Allah ya warkar da ita daga wata rashin lafiya da ta shafe kusan shekaru tara tana fama da ita.
Halima ta ce ta sha fuskantar barazanar rasa ranta a lokacin jinyar, amma bayan samun lafiya ta yanke shawarar sadaukar da rayuwarta wajen bautar Yesu Almasihu.
Ta ce sauyin da ta samu ba wai na lafiyar jiki kaɗai ba ne, har da sauyin rayuwa ta fuskar addini.
Jarumar ta kuma bayyana cewa nan ba da jimawa ba za ta fito fili ta bayar da cikakken shaidar yadda ta ce Allah ya yi amfani da Queen Belemzy Ministries (School of Power) wajen dawo mata da lafiya.
– Wakiliya





