Daga Wakiliya
Gwamnatin Ghana ta sanar da cewa za ta ɗauki mataki kan duk wata tashar talabijin da ke nuna fina-finan Najeriya ba tare da cikakken izini ba.
Mataimakin Shugaban Hukumar Kula da Masana’antar Fina-finai ta Ghana (NFA), James Gardiner, ya ce gwamnati na aiki tare da hukumomin sadarwa domin ƙirƙirar dokar da za ta soke lasisin duk tashoshin TV da suka karya ƙa’ida, kafin a tilasta musu sake neman sabbin lasisoshi.
James Gardiner ya bayyana hakan ne bayan wani furodusan fina-finai na Najeriya, Uchenna Mbunabo, ya zargi wasu tashoshin talabijin na Ghana da sauke fina-finan Nollywood daga YouTube tare da nuna su ba tare da izinin masu su ba.
A cewarsa, ana sa ran sabuwar dokar za ta fara aiki nan da shekarar 2027.
Tun da farko, fitattun jaruman Nollywood da suka haɗa da Bimbo Ademoye, Omoni Oboli, Mercy Johnson da Ruth Kadiri sun sha yin korafin cewa wasu tashoshin talabijin na Ghana na nuna fina-finansu ba tare da izini ba.





