Daga Wakiliya
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin ƙwace kaddarori 48 da aka kiyasta darajarsu ta kai Naira biliyan 213bn da Hukumar EFCC ta ce suna da alaƙa da tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), tare da mayar da su mallakin Gwamnatin Tarayya.
Alƙaliya Joyce Abdulmalik ta yanke hukuncin ne bayan ta ce EFCC ta gabatar da hujjojin da suka nuna ana zargin an mallaki kaddarorin ne da kuɗaɗen da ba su fito daga halastattun hanyoyin samun kuɗi ba, yayin da waɗanda suka ƙalubalanci ƙwacen suka kasa nuna sahihin asalin kuɗaɗen da aka yi amfani da su wajen sayen su.
Daga cikin manyan kaddarorin da kotun ta umarci a ƙwace akwai Rayhaan University da rassa da gine-ginenta a Jihar Kebbi, Rayhaan Radio, Rayhaan Agro Allied Factory, Azbir Arena, da otal-otal, gidaje, filaye, shaguna da sauran kadarori a Abuja, Kano da Kebbi.
Tun a ranar 6 ga Janairu, 2026, kotu ta fara bayar da umarnin ƙwace kadarorin na wucin gadi. Bayan EFCC ta wallafa sanarwar a jaridu domin bai wa masu ruwa da tsaki damar kare kansu, Abubakar Malami da wasu mutum 14 da suka haɗa da ‘yan uwansa da abokan hulɗarsa sun garzaya kotu suna ƙalubalantar umarnin.
Sai dai a hukuncin ƙarshe da aka yanke a ranar Laraba, kotun ta ce masu ƙalubalantar ƙwacen sun kasa gabatar da hujjojin da za su tabbatar da cewa an sayi kadarorin ne da kuɗaɗen da aka samu ta halastacciyar hanya. Saboda haka, kotun ta tabbatar da ƙwace dukkan kaddarorin 48 tare da mayar da su mallakin Gwamnatin Tarayya.
Me zaku ce?
LIKE | SHARE & FOLLOW => Wakiliya
DUBA COMMENT SECTION⤵️





