Wani mutum ya rasa ransa bayan an yi masa dukan tsiya sakamakon zargin cewa yana bibiyar matar wani a Jihar Kano.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa wanda ake zargin mijin matar ne ya shirya tarko domin kama mutumin. Bayan an kama shi, an yi masa jina-jina, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.
A cewar Rundunar, an kama mijin, matarsa da kuma wani mutum guda, kuma a halin yanzu suna tsare a hannun ‘yan sanda yayin da ake tuhumarsu da zargin kisan kai.
Rundunar ta ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu idan bincike ya kammala.




