Yara 3 cikin 4 a Najeriya ba sa iya karatu kafin su kai shekara 10 -inji Ministan Ilimi

Daga Wakiliya


Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa yara uku cikin huɗu a Najeriya ba sa iya karantawa tare da fahimtar rubutun da ya dace da shekarunsu kafin su kai shekara 10, lamarin da ta ce na nuna matsalar ilimi mai tsanani a ƙasar.

Ministan Ilimi, Olatunji Alausa, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin wani taro kan inganta sakamakon koyo ta hanyar amfani da fasahar zamani.

A cewarsa, Najeriya ba ta da wani zaɓi illa ta rungumi koyarwa ta hanyar fasahar zamani domin magance matsalar, yana mai cewa ci gaba da dogaro da tsohuwar hanyar koyarwa kaɗai ba zai wadatar ba.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya ta samar da dandamalin koyon ilimi na zamani kamar Nigeria Learning Passport da wasu, amma amfani da su har yanzu bai kai yadda ake buƙata ba.

Ministan ya bayyana cewa duk da samun masu amfani kusan miliyan 2.3 a Nigeria Learning Passport, adadin ya yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da kimanin ɗalibai miliyan 67 da ke makarantun firamare da sakandare a faɗin Najeriya.

Ya buƙaci gwamnatocin jihohi da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi su ƙara amfani da waɗannan dandamali domin inganta koyarwa da rage ƙarancin ƙwararrun malamai, musamman a darussan Lissafi, Turanci, Kimiyyar Jiki da Kimiyyar Sinadarai.

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img