Daga Wakiliya
Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya zaɓi tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, a matsayin mataimakin takararsa ta shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta ce ta riga ta miƙa sunaye da bayanan Atiku da Amaechi cikin nasara zuwa shafin karɓar sunayen ‘yan takara na Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC).
Mai magana da yawun jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanar da hakan a shafinsa na X, inda ya ce matakin na nuna yadda ADC ke ci gaba da shirye-shiryenta domin babban zaɓen 2027.
A cewarsa, jam’iyyar na da burin bai wa ‘yan Najeriya wata madadin gwamnati da ta ginu kan ƙwarewa, haɗin kai da kuma sabunta ƙasa.





