Daga Wakiliya
Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya buƙaci al’ummar jihar su bai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kashi 98 cikin 100 na kuri’unsu a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Uba Sani ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin ƙaddamar da ayyukan tituna guda 11 a ƙananan hukumomin Zariya da Sabon Gari. Ya ce Shugaba Tinubu ya nuna goyon baya sosai ga ayyukan raya ƙasa a Kaduna, musamman gina tituna da sauran manyan ayyukan more rayuwa.
Gwamnan ya ce gwamnatin tarayya ta kuma zaɓi Kaduna da Legas ne kaɗai domin aiwatar da aikin layin dogo na cikin birni (Light Rail), inda ya bayyana cewa aikin na Kaduna mai darajar tiriliyan N1 zai fara cikin watanni biyu masu zuwa, bayan an riga an tura ‘yan kwangila wuraren aiki.
Ya kuma sanar da cewa za a yi bikin aza harsashin titin Mando zuwa Birnin Gwari cikin makon nan, yana mai cewa Shugaba Tinubu ya riga ya ware sama da biliyan N100 domin aikin.
Uba Sani ya ce irin waɗannan ayyuka sun sa ya zama wajibi al’ummar Kaduna su mayar da alherin da shugaban ƙasa ya yi musu ta hanyar sake zaɓensa a 2027.
Hakazalika, gwamnan ya yi kira ga al’ummar Zariya su sake zaɓen Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, tare da goyon bayan ‘yan takarar jam’iyyar APC a zaɓe mai zuwa.
A cewarsa, ayyukan tituna guda 11 da aka ƙaddamar a Zariya da Sabon Gari za a kammala su cikin watanni biyar, yayin da gwamnatinsa ta fara ayyukan tituna sama da 150 masu tsawon fiye da kilomita 1,355, inda yawancinsu tuni aka kammala.





