Daga Wakiliya
Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta haɗa karatun Larabci cikin manhajar ilimin Najeriya domin bai wa waɗanda suka yi karatu a ƙasashen Larabawa cikakkiyar damar a amince da takardun karatunsu kamar sauran masu digiri.
Bala Mohammed ya bayyana hakan ne yayin da ya karÉ“i baÆ™uncin tawagar ‘yan kasuwar Saudiyya da shugabannin É—aliban Najeriya da ke karatu a jami’o’in Saudiyya, Æ™arÆ™ashin jagorancin Daraktan Cibiyar Nazarin Sunnah a Afirka, Dakta Shuaibu Abubakar Idris, a Fadar Gwamnatin Bauchi.
Gwamnan ya nuna damuwa kan abin da ya kira raguwar kulawa da gadon ilimin Larabci a Arewacin Najeriya, yana mai cewa yankin ya daÉ—e yana da alaÆ™a ta ilimi, addini da al’adu da Æ™asashen Larabawa.
Ya kuma yi kira da a farfaɗo da tsohuwar Kwalejin Larabci ta Alkaleri, wadda ya ce ta taɓa yin fice amma aka yi watsi da ita a gwamnatocin da suka gabata.
A nasa jawabin, Dakta Shuaibu Abubakar Idris ya ce sun kai ziyarar ne domin gabatar da wasu ‘yan kasuwar Saudiyya masu sha’awar zuba jari a Jihar Bauchi, tare da bayyana ayyukan cibiyar da kuma irin tallafin da take bai wa É—aliban Bauchi da ke karatu a Saudiyya.
A nasu ɓangaren, wakilan ɗaliban Najeriya da ke karatu a Saudiyya sun gode wa Bala Mohammed bisa goyon bayan da yake ba su, tare da alƙawarin amfani da ilimi da ƙwarewar da suka samu wajen bunƙasa Bauchi da Najeriya bayan kammala karatunsu.





