Daga Wakiliya
“Wa Ya Ce Mijinki Bai Son Matarsa Ta Farko Ba?” – Waraka Temple Ta Gargaɗi Mata Masu Shirin Zama Matan Aure Na Biyu
Mashahuriyar mai ba da shawara kan zamantakewar aure da iyali, Waraka Temple, ta yi gargaɗi ga mata masu shirin zama mata na biyu da kada su shiga gidan miji da girman kai ko tunanin cewa mijin ya daina son matarsa ta farko.
Da take magana a wata tattaunawa da aka yi da ita a shirin Fact News Hausa Podcast, Waraka Temple ta ce wasu sabbin amaren kan shiga gidan aure da tunanin cewa kasancewar namiji ya aure su na nufin ya watsar da matarsa ta farko, alhali hakan ba gaskiya ba ne.
“Wa ya gaya miki cewa bai son matarsa ta farko? Maza dai sun iya nuna abubuwa ta wata hanya,” in ji ta.
Ta ce wasu sabbin mata kan yi ƙoƙarin burge mijinsu fiye da kima ta hanyar ɗaukar nauyin ayyuka masu wahala kamar wanke mota da sauran hidimomi da ba za su iya ci gaba da yi ba, domin kawai su nuna sun fi matar farko.
Waraka Temple ta ƙara da cewa matsayin matar farko ba abu ne mai sauƙin gogewa ba, domin sau da yawa ya samo asali ne daga shekaru na haƙuri, zaman tare da kuma ƙaunar da aka gina a cikin iyali. Saboda haka, ta shawarci mata masu shiga gidan miji a matsayin mata na biyu da su kasance masu tawali’u, nutsuwa da tsoron Allah, maimakon neman gogayya da matar farko.
A nasa bangaren, ɗaya daga cikin masu gabatar da shirin, A. Ladan Zamani, ya jaddada cewa babban nauyi yana kan miji wajen tabbatar da adalci tsakanin matansa.
Ya ce duk da cewa addini da al’ada sun amince da auren fiye da mace ɗaya, hakan yana tare da sharadin yin adalci da kyakkyawan tafiyar da gida.
“Idan miji ba zai iya yin adalci tsakanin matansa ba, to manufar ƙara aure ta rasa ginshiƙinta,” in ji A. Ladan Zamani.
Tattaunawar ta jawo ce-ce-ku-ce da martani daga al’ummar Hausawa, inda da dama ke ganin ta sake haskaka muhimmancin mutunta juna, hakuri da kuma fahimtar juna a gidajen da ake zaman aure fiye da mace ɗaya.





