Daga Wakiliya
Wani bincike da ya shafe shekaru biyar, wanda Petroleum Technology Development Fund (PTDF) ya gudanar tare da Jami’ar Jos, ya gano alamun da ke nuna akwai yiwuwar samun man fetur da iskar gas a wasu sassan Jihar Plateau.
A wajen gabatar da sakamakon binciken a Jami’ar Jos, Farfesa Nuhu Kadai Samaila ya ce binciken ya tabbatar da cewa yankin Shendam na da siffofin kasa da ke nuna yiwuwar samar da sinadaran man fetur.
Ya bayyana cewa abin da binciken ya fi tabbatarwa a halin yanzu shi ne akwai yiwuwar iskar gas, yayin da kuma aka samu wasu alamun da ke nuna yiwuwar samun danyen mai, musamman a yankunan Langtang ta Arewa da Langtang ta Kudu.
A cewarsa, ana bukatar a gudanar da binciken seismic survey tare da haÉ—in gwiwar NNPCL domin tantance yawan albarkatun da kuma ko za su iya zama abin hakowa ta kasuwanci.
Baya ga man fetur da iskar gas, binciken ya kuma gano ma’adinan barite da kuma wasu albarkatun makamashin zafi daga karkashin kasa (hydrothermal energy) da za su iya taimakawa wajen samar da wutar lantarki.
Shugaban PTDF, Farfesa Shuaibu Shehu Aliyu, ya bukaci jami’o’in Najeriya su mayar da hankali kan binciken da zai kai ga samar da hanyoyin jawo zuba jari da ci gaban masana’antu, yayin da Shugaban Jami’ar Jos, Farfesa Tanko Ishaya, ya ce binciken ya nuna muhimmancin haÉ—in gwiwa tsakanin jami’o’i da masana’antu wajen bunÆ™asa tattalin arzikin Æ™asa.
Rahoton ya ce sakamakon wannan bincike zai taimaka wajen jagorantar ƙarin bincike da yanke shawara kan yiwuwar hako man fetur da iskar gas a Plateau da sauran yankunan Benue Trough.





