Daga Wakiliya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Independent Corrupt Practices and Other Related Offences Commission ta gudanar da cikakken bincike kan wata ƙungiya da ke kiran kanta Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC), wadda gwamnatin tarayya ta ce ba ta taɓa kafa ta ba.
A cikin sanarwar da mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Talata, an ce shugaban ya ba ICPC wa’adin kwanaki 30 ta kammala binciken tare da miƙa masa rahoto.
Sanarwar ta ce wani mutum mai suna Adeniyi Adeyemi Matthew ya riƙa gabatar da kansa a matsayin Darakta Janar na PFIPC, tare da iƙirarin cewa shugaban ƙasa ne ya naɗa shi, duk da cewa babu wata doka ko amincewar gwamnati da ta kafa irin wannan hukuma.
An ce binciken zai haɗa da zargin ƙirƙirar takardun naɗi na bogi, amfani da sunan shugaban ƙasa wajen neman sahalewar hukumomi da tallafin diflomasiyya, da kuma buɗe asusun banki da sunayen wasu hukumomin gwamnati ta hanyar amfani da takardun da ake zargin na bogi ne.
Haka kuma, shugaban ya umarci ICPC ta binciki duk wani mutum ko hukuma da ake zargin ta taimaka wajen aiwatar da wannan shiri, tare da gano giɓin da ke cikin tsarin gwamnati da ya ba da damar faruwar lamarin, domin ba da shawarwarin yadda za a hana sake aukuwar irin haka.
Tinubu ya ce dole ne a kare martabar Fadar Shugaban Ƙasa da hukumomin gwamnatin tarayya daga masu amfani da jabun takardu, satar suna da kuma kwaikwayon muƙaman gwamnati, yana mai umartar a hukunta duk wanda bincike ya tabbatar da laifinsa bisa tanadin doka.





