Sule Lamido Ya Yiwa Pantami Gori Kan Yadda A Baya Ya Rika Kiran PDP “Jam’iyyar Kafirai”


Daga Wakiliya

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya soki tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Isa Ali Pantami, inda ya tuna masa cewa a baya ya taba kiran PDP da “jam’iyyar kafirai.”

Lamido ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga jihohin Gombe, Bauchi, Kano, Yobe da Jigawa a gidansa da ke Bamaina, Jihar Jigawa.

A cewarsa, duk da suka da zarge-zargen da aka dade ana yi wa PDP, har ma da kiranta “jam’iyyar kafirai”, bai taɓa barin jam’iyyar ba bayan ya sauka daga mulki.

Ya kuma yi ikirarin cewa bayan zaɓen 2015, manyan jagororin APC sun nemi ya koma jam’iyyarsu, amma ya ƙi, yana mai cewa ba zai bar jam’iyyar da ta ba shi damar zama Ministan Harkokin Wajen Najeriya da kuma Gwamnan Jigawa har sau biyu ba.

Lamido ya kuma yi zargin cewa Pantami, lokacin da yake Babban Limamin Masallacin Juma’a na ATBU, ya kasance yana wa’azi tare da addu’ar Allah Ya kawo ƙarshen PDP, yana kiranta “jam’iyyar kafirai.”

Ya ƙara da cewa daga baya Pantami ya shiga PDP bayan da bai samu tikitin takarar gwamnan APC a Jihar Gombe ba, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta.

Wannan na zuwa ne yayin da harkokin siyasa da sauya sheƙar ‘yan siyasa ke ƙara zafafa gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img