Shugaban Nicaragua Ya Ce Ba Za a Sake Gudanar da Zaɓe a Ƙasar Ba

Daga Wakiliya

Shugaban ƙasar Nicaragua, Daniel Ortega, ya bayyana cewa ba za a sake gudanar da wani zaɓe a ƙasar ba, yana mai cewa gwamnatinsa na shirin samar da dokokin da za su hana abin da ya kira yunƙurin juyin mulki da cin amanar ƙasa.

Ortega, mai shekaru 80, ya yi wannan jawabi ne yayin bikin cika shekara 47 da juyin juya halin Sandinista da ya hambarar da gwamnatin Anastasio Somoza a shekarar 1979.

Tun daga shekarar 2007, Daniel Ortega ke mulkin Nicaragua, kuma an sha zarginsa da sauya dokoki domin tsawaita zamansa kan mulki.

A bara ma, an tsawaita wa’adin shugaban ƙasa zuwa shekara shida tare da ɗaga matarsa, Rosario Murillo, daga mataimakiyar shugaban ƙasa zuwa matsayin karamar shugabar ƙasa (Co-President).

Kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun dade suna zargin gwamnatin Ortega da murƙushe ‘yan adawa, kama masu fafutuka, ‘yan jarida da jagororin siyasa, musamman a zaɓukan shekarun 2011, 2016 da 2021.

A jawabinsa, Ortega ya ce za su yi aiki da Majalisar Dokoki wajen samar da dokokin da za su “gina katanga” domin hana waɗanda ya kira masu shirya juyin mulki sake samun damar karɓar mulki ta hanyar zaɓe.Haka kuma, Ortega ya soki gwamnatin Amurka kan abin da ya yi iƙirarin cewa ta aikata wa shugaban Venezuela, Nicolás Maduro, yana zargin Amurka da kai farmaki fadar shugaban ƙasa tare da kama Maduro.

Sai dai babu wata hujja mai zaman kanta da ta tabbatar da wannan iƙirari.

DA DUMI-DUMI

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Kanun Labarai

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img