Daga Wakiliya
Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Elijah Ayodele, ya ce ya hango sauye-sauye a manyan muƙaman gwamnati kafin zaɓen 2027, inda ya yi hasashen za a samu sabon Mataimakin Shugaban Ƙasa, sabon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), sabon Shugaban Majalisar Dattawa da kuma sabon Ministan Tarayya.
Primate Ayodele ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da littafinsa na hasashe na shekara-shekara mai taken Warnings To The Nations karo na 32, a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedkwatar cocinsa da ke Lagos.
Malamin ya kuma yi iƙirarin cewa akwai shirye-shiryen da ake yi a ɓoye domin yin maguɗin zaɓen 2027, tare da cewa wani tsohon Shugaban Ƙasa ba zai goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba.
Haka kuma, Primate Ayodele ya ce yankin Arewa zai nuna rashin jin daɗi ga Shugaba Tinubu kafin zaɓen 2027, yana mai cewa nasarar Shugaban Ƙasar ba tabbas sai idan ya ɗauki wasu matakai masu muhimmanci.
Baya ga haka, ya yi hasashen cewa Gwamnan Jihar Ademola Adeleke zai lashe zaɓen gwamnan Osun mai zuwa, amma ya gargade shi da ya sa ido sosai kan yadda zaɓen zai gudana, yana zargin ana matsa wa hukumar INEC lamba kan gudanar da zaɓen.
Wakiliya ta lura cewa waɗannan kalamai hasashe ne na Primate Ayodele, kuma ba su da wata hujjar hukuma da ta tabbatar da faruwarsu.





