Maraban JOS:  Amnesty Ta Zargi ‘Yan Sanda da Yiwuwar Rufe Gaskiya a Kisan Ummulkhair



Daga Wakiliya

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta buÆ™aci gwamnatin Najeriya ta kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin gano gaskiyar abin da ya faru a kisan gillar da aka yi wa Ummulkhair, malama kuma uwa ga yara biyar.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta bayyana cewa ba za a iya dogaro da binciken da rundunar ‘yan sanda ta ce tana yi ba, musamman ganin cewa akwai zarge-zargen cewa wasu jami’an ‘yan sanda sun taka rawa wajen mika marigayiyar ga taron mutanen da suka kashe ta.

Amnesty ta ce shaidu sun bayyana mata cewa lokacin da jama’a suka mamaye ofishin ‘yan sanda a ranar 21 ga Yuni, jami’an da ke bakin aiki sun fitar da Ummulkhair daga wurin da ake bata kariya, suka cire mata hijabi sannan suka mika ta ga masu tarzoma, inda suka kashe ta tare da kona gawarta.

Ƙungiyar ta ce ci gaba da yawaitar kashe-kashen gilla a Najeriya alama ce ta gazawar gwamnati wajen kare rayuka da tabbatar da adalci. Ta kuma zargi jami’an tsaro da gaza bincike da hukunta masu hannu a irin waɗannan laifuka a lokuta da dama.

Amnesty International ta jaddada cewa dole ne a gudanar da bincike na gaskiya, adalci da cikakken ‘yanci domin tabbatar da an hukunta duk wanda aka samu da hannu a wannan aika-aika.

Rahoton – Wakiliya

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, KuÉ—in Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, KuÉ—in Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe ZaÉ“en 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, KuÉ—in Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, KuÉ—in Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe ZaÉ“en 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin É—in Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin É—in Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya ÆŠauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img