Daga Wakiliya
Majalisar Dattawan Najeriya ta ce kudirin kafa ‘Yan Sandan Jihohi ba na siyasa ba ne, illa matakin da aka dauka domin magance matsalar tsaro da ke addabar kasar.
Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga masu sukar kudirin, ciki har da Peter Obi da Hakeem Baba-Ahmed, wadanda suka nuna damuwa kan yiwuwar amfani da rundunar wajen cimma muradun siyasa.
Bamidele ya ce kudirin ya samo asali ne daga bukatar kasa, kuma an shafe lokaci ana tattaunawa da tuntubar masu ruwa da tsaki da suka hada da gwamnoni, rundunar ‘yan sanda, da majalisun dokokin jihohi, tare da gudanar da sauraron ra’ayin jama’a a dukkan shiyyoyin kasar.
Ya kara da cewa an saka tanade-tanaden da za su tabbatar da sa ido da hana duk wani amfani da rundunar ta hanyar da ba ta dace ba.
A cewarsa, sanatoci 84 cikin 109 ne suka amince da kudirin a Majalisar Dattawa, lamarin da ya nuna cewa kudirin ya samu goyon bayan ‘yan majalisa daga jam’iyyu daban-daban.
Bamidele ya jaddada cewa batun tsaron kasa ya kamata ya wuce siyasa, yana mai kira ga jam’iyyun adawa da su bayar da shawarwari masu amfani maimakon su tsaya kan suka kawai.





